Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Tawagar Masu Yi Wa Maniyyata Hidima Za Ta Tashi Zuwa Saudiyya Afrika
  • ADC Ta Kaucewa INEC Ta Gudanar Da Babban Taro Labarai
  • Za A Cigaba Da Tattaunawa Domin Kawo Karshen Yakin Gabas Ta Tsakiya Amurka
  • Gamayyar ADC Ta Bukaci Shugaban INEC Ya Yi Murabus Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Ƙungiyar ‘Yan Jarida (NUJ) A Bauchi Ta Yi Allah Wadai Da Mummunan Harin Da Jami’an ‘Yan Sanda Suka Kai Wa Daya Daga Cikin Mambobinta Labarai

Gwamnatin Filato Ta Gurfanar Da Maharan Rukuba A Kotu
Published: April 22, 2026 at 5:31 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Gwamnatin jihar Filato ta gurfanar da mutane biyar a gaban kotu da take zargi da kai hari da kisan mutane fiye da talatin a Anguwar Rukuba dake karamar hukumar Jos ta Arewa.

A ranar Jumma’ar da ta gabata ne gwamnatin jihar Filato ta shigar da karar wassu mutane biyar a gaban kotu, wanda jami’an tsaro na farin kaya ta DSS suka kama, bisa zargin kashe mutane fiye da talatin a karshen watan Maris na wannan shekara, a Anguwar Rukuba dake karamar hukumar Jos ta Arewa.

Gwamnatin ta shigar da karar mutane hudu daga cikinsu kan laifin ta’addanci, yayinda mutum guda ake tuhumarsa da laifin hadin baki, kisa, mallakar makamai da safarar makamai da albarusai ba bisa ka’ida ba.

Da yake gurfanar da wadanda ake zargin a gaban kotu, babban lauyan jihar, Philemon Audu Daffi yace laifin da mutanen suka aikata ya saba wa sashe na 269 da sashe na 270 na dokar Penal code na jihar Filato.

Rahoton da kakakin rundunar dake aikin wazadda zaman lafiya a jihar Filato ta Operation Enduring Peace, Chinonso Oteh ya aike wa manema labarai, bai bayyana ranar da za’a ci gaba da sauraron karar ba.

A halin da ake ciki dai, yayinda zaman lafiya ya dawo cikin birnin Jos, wassu da suka tsira da lafiyarsu, a lokacin tashin hankalin, sun bayyana cewa mabiya addinan da ba nasu ba sune suka boye su, don kar a hallaka su.

Malama Martha Kura tace ta gamu da fusatattun matasa ne yayinda ta fito kasuwa, amma al’ummar musulmi dake wurin suka kareta.

Shima Alhaji Nasiru Muhammad Ali wanda rikicin ya rutsa da shi a unguwar Eto-Baba, dake kusa da Anguwar Rukuba yace kirista ne suka boye shi.

Al’ummar jihar Filato dake son zaman lafiya dai suna kan fadakar da jama’a muhimmancin kyakkyawar hulda da zamantakewa don samun ci gaba.

Ga Rahoton Zainab Babaji Daga Jos

https://gtahausa.com/wp-content/uploads/2026/04/AUD-20260422-WA0056.mp3
Afrika, Najeriya, Tsaro

Post navigation

Previous Post: Gwamnatin Najeriya Ta Tallafa Wa ’Yan Sanda Da Motoci
Next Post: Sanata Barau Ya Raba Motoci Da Babura Ga Al’ummar Kano Ta Arewa

Karin Labarai Masu Alaka

Hawan Nasarawa A Jihar Kano Afrika
Hukumar Upper Benue Zata Inganta Noma A Dadinkowa Afrika
Shugaba Tinubu Ya Turawa Majalisa Sunayen Mutane Biyun Da Zasu Shugabanci Sashin Albarkatun Mai Labarai
Iran Tace Jakadan Kasar Ta A Lebanon Zai Cigaba Da Zama A Beirut Afrika
Kotun Uganda Tayi Watsi Da Karar Hukumomin Kasar Afrika
Kungiyar HPV A Jihar Gombe Ta Jagoranci Yaki Da Karuwar Cutar Daji Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Tawagar Masu Yi Wa Maniyyata Hidima Za Ta Tashi Zuwa Saudiyya
  • Shugaba Tinubu Ya Ware Kudade Domin Bunkasa Rayuwar ‘Yan Najeriya
  • Sanata Barau Ya Raba Motoci Da Babura Ga Al’ummar Kano Ta Arewa
  • Gwamnatin Filato Ta Gurfanar Da Maharan Rukuba A Kotu
  • Gwamnatin Najeriya Ta Tallafa Wa ’Yan Sanda Da Motoci

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Shugaba Trump Yace Amurka Zata Janye Yaki Da Iran Afrika
  • Shugaba Tinubu Ya Kara Aika Sunayen Jakadu Ga Majalisa Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Alaka Na Cigaba Da Kamari Tsakanin Rwanda Da Barundi Labarai
  • Dakarun Tsaron Ruwan Amurka Sunfara Killace Hanyoyi Amurka
  • Iran Zata Kawo Karshen Yaki Da Isra’ila Da Amurka Amurka
  • Hafsan Sojin Najeriya: Samar Da Sabbin Wajen Horas Da Sojoji Zai Inganta Tsaro Tsaro
  • Ana Gudanar Da Zaben Shugaban Kasa A Djibouti Yau Juma’a Afrika
  • Hukumar Tsaro Ta DSS Ta Aika Sammaci Dr. Yusuf Baba-Ahmed Labarai
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.