Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Likitoci Masu Neman Kwarewa Zasu Shiga Yakin Aiki Afrika
  • Gwamnan Gombe Ya Yaba Da Hikima Da Jagorancin Sarkin Gombe A Shekaru 12 Na Jagoranci Afrika
  • JEI Da Abokan Hulɗar Sun Gudanar Da Aikin Shuka Itatuwa Domin Bikin Ranar Muhalli Ta Duniya Afrika
  • Za’ayi Jana’izar Marigayi Ali Khamenei a Tehran, Qom da Mashhad Afrika
  • An Fara Dawo Da Alhazain Najeriya Gida Afrika

Gwamnatin Filato Ta Gurfanar Da Maharan Rukuba A Kotu
Published: April 22, 2026 at 5:31 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Gwamnatin jihar Filato ta gurfanar da mutane biyar a gaban kotu da take zargi da kai hari da kisan mutane fiye da talatin a Anguwar Rukuba dake karamar hukumar Jos ta Arewa.

A ranar Jumma’ar da ta gabata ne gwamnatin jihar Filato ta shigar da karar wassu mutane biyar a gaban kotu, wanda jami’an tsaro na farin kaya ta DSS suka kama, bisa zargin kashe mutane fiye da talatin a karshen watan Maris na wannan shekara, a Anguwar Rukuba dake karamar hukumar Jos ta Arewa.

Gwamnatin ta shigar da karar mutane hudu daga cikinsu kan laifin ta’addanci, yayinda mutum guda ake tuhumarsa da laifin hadin baki, kisa, mallakar makamai da safarar makamai da albarusai ba bisa ka’ida ba.

Da yake gurfanar da wadanda ake zargin a gaban kotu, babban lauyan jihar, Philemon Audu Daffi yace laifin da mutanen suka aikata ya saba wa sashe na 269 da sashe na 270 na dokar Penal code na jihar Filato.

Rahoton da kakakin rundunar dake aikin wazadda zaman lafiya a jihar Filato ta Operation Enduring Peace, Chinonso Oteh ya aike wa manema labarai, bai bayyana ranar da za’a ci gaba da sauraron karar ba.

A halin da ake ciki dai, yayinda zaman lafiya ya dawo cikin birnin Jos, wassu da suka tsira da lafiyarsu, a lokacin tashin hankalin, sun bayyana cewa mabiya addinan da ba nasu ba sune suka boye su, don kar a hallaka su.

Malama Martha Kura tace ta gamu da fusatattun matasa ne yayinda ta fito kasuwa, amma al’ummar musulmi dake wurin suka kareta.

Shima Alhaji Nasiru Muhammad Ali wanda rikicin ya rutsa da shi a unguwar Eto-Baba, dake kusa da Anguwar Rukuba yace kirista ne suka boye shi.

Al’ummar jihar Filato dake son zaman lafiya dai suna kan fadakar da jama’a muhimmancin kyakkyawar hulda da zamantakewa don samun ci gaba.

Ga Rahoton Zainab Babaji Daga Jos

https://gtahausa.com/wp-content/uploads/2026/04/AUD-20260422-WA0056.mp3
Afrika, Najeriya, Tsaro

Post navigation

Previous Post: Gwamnatin Najeriya Ta Tallafa Wa ’Yan Sanda Da Motoci
Next Post: Sanata Barau Ya Raba Motoci Da Babura Ga Al’ummar Kano Ta Arewa

Karin Labarai Masu Alaka

Tinubu Ya Sayi Fom Din Takarar Shugaban Kasa Afrika
Sakataren Tsaron Amurka Ya Kori Shugaban Sojin Kasar Amurka
China Da Jamhuriyar Dimokraɗiyya Kwango Sun Kulla Yarjejeniya Afrika
An Kai Hari Kan Masu Hakar Ma’adanai A Kasar Mali Tsaro
PDP Ta Tsayar da Goodluck Jonathan Takarar Shugaban Kasa Afrika
Gwamnatin Tarayya Ta Cire Sharadin Rubuta UTME Ga Masu Neman Shiga Kwalejojin Ilimi Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Likitoci Masu Neman Kwarewa Zasu Shiga Yakin Aiki
  • Gwamnan Gombe Ya Yaba Da Hikima Da Jagorancin Sarkin Gombe A Shekaru 12 Na Jagoranci
  • JEI Da Abokan Hulɗar Sun Gudanar Da Aikin Shuka Itatuwa Domin Bikin Ranar Muhalli Ta Duniya
  • Mourinho Ya ƙara Ta’azzara Takaddamarsa Da Hukumomin ƙwallon ƙafar Turkiyya
  • Za’ayi Jana’izar Marigayi Ali Khamenei a Tehran, Qom da Mashhad

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Fafaroma Leo Yayi Allah Wadai Bisa Karuwar Yake Yaken Gabas Ta Tsakiya Amurka
  • Isra’ila Ta Kai Hari Cibiyar Makamashin Nukiliyar Iran Afrika
  • Yakin Gabas Ta Tsakiya Ya Kawo Cikas Ga Cinikin Nama A Kenya Afrika
  • ‘Yan Gudun Hijira A Kasar Libya Suna Fuskantar Cin Zarafi Afrika
  • Likitoci Masu Neman Kwarewa Zasu Shiga Yakin Aiki Afrika
  • Anyi Rashin Mutane Da Yawa Yayinda Bom Ya Fashe Ana Sallar Magariba Maiduguri Labarai
  • Trump: Isra’ila Ta Daina Kai Hari Ga Duk Cibiyar Iskar Gas Afrika
  • Farashin Danyen Mai Da Iskar Gas Ya Tashi Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.