Kotu ta bayar da belin Nasir El-Rufai kan Naira miliyan 100
Wata babbar kotu da ke Abuja a Najeriya bayar da beli ga tsohon gwamnan jihar Kaduna, Nasir El-Rufai, kan zargin karan tsaye ga tsaron kasa da ake yi masa.
Mai shari’a Joyce Abdulmalik, yayin yanke hukunci kan buƙatar beli a ranar Litinin, ta gindaya wasu tsauraran sharuɗɗa da El-Rufai zai cika kafin a sake shi.
Kotun ta umarce shi da ya kawo mutum guda da zai tsaya masa beli da adadin kuɗin iri ɗaya.
Kotun ta ce dole ne wanda zai tsaya masa ya kasance mazaunin yankin Maitama ko Asokoro a Abuja, sannan ya ajiye asalin takardar mallakar fili ko gida a ma’ajiyar kotu.
Haka kuma, wanda zai tsaya belin dole ne ya kasance ma’aikacin gwamnatin tarayya mai matsayi bai gaza mataki na 17 ba, tare da gabatar da shaidar biyan albashi na akalla watanni uku, wanda manajan bankinsa a yankin kotun ya tabbatar.
Kotun ta kuma umurci wanda zai tsaya masa ya rantse da takardar bayyana kadarori, ya sanya hannu kan yarjejeniyar beli tare da gabatar da sabon hoton fasfo a ma’ajiyar kotu.
A cikin sharuɗɗan belin, an umurci El-Rufai da ya miƙa duk wasu ingantattun fasfo na ƙasashen waje ga kotu.
Kotun ta kuma buƙaci a gabatar da wasiƙar tabbatarwa daga sashen aikin wanda ya tsaya belin, tare da takardar biyan haraji ta watanni shida da suka gabata.
Mai shari’a Abdulmalik ta kuma umurci wanda ake tuhuma da ya riƙa zuwa hedikwatar Hukumar Tsaro ta DSS a kowace Juma’ar ƙarshe ta wata da ƙarfe 10 na safe domin sanya hannu a rajistar halarta har sai an kammala shari’ar.
Alƙaliyar ta yi gargaɗin cewa rashin bin waɗannan sharuɗɗa zai sa a soke belin kai tsaye.
Kotun ta ƙara umurtar El-Rufai da ya gabatar da wasiƙar shaida daga Shugaban Majalisar Sarakunan Gargajiya ta Kaduna.
Haka kuma, kotun ta ba da umarnin a gaggauta sauraron shari’ar da gwamnatin Najeriya ta shigar a kansa.


