Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Najeriya Da Jamus Sun Kulla Yarjejeniyar Zuba Jari Afrika
  • Zaben Fidda Gwani Ya Gudana Lafiya A Jihar Gombe Afrika
  • Sojin Najeriya Da Amurka Sun Hallaka Jagoran ISIS Afrika
  • Hukumar ‘Yan Sanda Tayi Yarjejeniya Da ‘Yan Takara A Gombe Afrika
  • Hukumomin Bada Agaji Sun Fadakar Da Al’ummar Jihar Gombe Afrika

Kotu Ta Bada Belin Nasiru El Rufai
Published: May 18, 2026 at 10:21 AM | By: Aliyu Bala Gerengi | Updated: May 18, 2026

Kotu ta bayar da belin Nasir El-Rufai kan Naira miliyan 100

Wata babbar kotu da ke Abuja a Najeriya bayar da beli ga tsohon gwamnan jihar Kaduna, Nasir El-Rufai, kan zargin karan tsaye ga tsaron kasa da ake yi masa.

Mai shari’a Joyce Abdulmalik, yayin yanke hukunci kan buƙatar beli a ranar Litinin, ta gindaya wasu tsauraran sharuɗɗa da El-Rufai zai cika kafin a sake shi.

Kotun ta umarce shi da ya kawo mutum guda da zai tsaya masa beli da adadin kuɗin iri ɗaya.

Kotun ta ce dole ne wanda zai tsaya masa ya kasance mazaunin yankin Maitama ko Asokoro a Abuja, sannan ya ajiye asalin takardar mallakar fili ko gida a ma’ajiyar kotu.

Haka kuma, wanda zai tsaya belin dole ne ya kasance ma’aikacin gwamnatin tarayya mai matsayi bai gaza mataki na 17 ba, tare da gabatar da shaidar biyan albashi na akalla watanni uku, wanda manajan bankinsa a yankin kotun ya tabbatar.

Kotun ta kuma umurci wanda zai tsaya masa ya rantse da takardar bayyana kadarori, ya sanya hannu kan yarjejeniyar beli tare da gabatar da sabon hoton fasfo a ma’ajiyar kotu.

A cikin sharuɗɗan belin, an umurci El-Rufai da ya miƙa duk wasu ingantattun fasfo na ƙasashen waje ga kotu.

Kotun ta kuma buƙaci a gabatar da wasiƙar tabbatarwa daga sashen aikin wanda ya tsaya belin, tare da takardar biyan haraji ta watanni shida da suka gabata.

Mai shari’a Abdulmalik ta kuma umurci wanda ake tuhuma da ya riƙa zuwa hedikwatar Hukumar Tsaro ta DSS a kowace Juma’ar ƙarshe ta wata da ƙarfe 10 na safe domin sanya hannu a rajistar halarta har sai an kammala shari’ar.

Alƙaliyar ta yi gargaɗin cewa rashin bin waɗannan sharuɗɗa zai sa a soke belin kai tsaye.

Kotun ta ƙara umurtar El-Rufai da ya gabatar da wasiƙar shaida daga Shugaban Majalisar Sarakunan Gargajiya ta Kaduna.

Haka kuma, kotun ta ba da umarnin a gaggauta sauraron shari’ar da gwamnatin Najeriya ta shigar a kansa.

Afrika, Labarai, Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu, Najeriya, Siyasa

Post navigation

Previous Post: Najeriya Da Jamus Sun Kulla Yarjejeniyar Zuba Jari

Karin Labarai Masu Alaka

Shugabar Kungiyar Cinikayya Ta Duniya Ta Bukaci Kasashe Su Gyara Harkokin Cinikayya Afrika
Jami’ai Daga Amurka Sunce Yakin Amurka Da Iran Zaizo Karshe Amurka
Najeriya Ta Bawa Dan Takarar Guinea-Bissau Mafaka Afrika
Farashin Mai Ya Cigaba Da Tashi Afrika
Tsohon Alkalin Alkalai A Najeriya Ya Rasu Yana Da Shekaru 71 Labarai
Shugaban Amurka Yace Zayyi Wahala A Cimma Yarjejeniya Tsakanin Isra’ila, Amurka Da Iran Amurka

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Kotu Ta Bada Belin Nasiru El Rufai
  • Najeriya Da Jamus Sun Kulla Yarjejeniyar Zuba Jari
  • Zaben Fidda Gwani Ya Gudana Lafiya A Jihar Gombe
  • Sojin Najeriya Da Amurka Sun Hallaka Jagoran ISIS
  • Hukumar ‘Yan Sanda Tayi Yarjejeniya Da ‘Yan Takara A Gombe

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Kotun Amurka Ta Soke Harajin Fito Da Shugaba Trump Ya Kakabawa Kayan Kasashen Waje Amurka
  • Burkina Faso Ta Sako Jami’an Rundunar Sojin Saman Najeriya 11 Da Aka Tsare Tsaro
  • Jirgi Marar Matuka Yayi Luguden Wutan A Abu Dhabi Afrika
  • Gwamnatin Sokoto Tabada Umarnin Biyan Albashin Watan Fabrairu Labarai
  • Shugaba Tinubu Ya Taya Musulmai Murnar Sallah, Tare Da Kira Zuwa Ga Kishin Kasa Afrika
  • Zulum Ya Rushe Majalisar Zartarwa Ta Jihar Borno Afrika
  • An Kafa Majalisar Kotun Sulhu Ta Kano Labarai
  • Rikici Ya Lafa A Kasar Iran Bayan Daukar Matakai Labarai
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.