Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Najeriya Ta Dauki Hayan Amurkawa Don Kyautata Alaka Da Trump Game Da Kisan Kiristoci Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnatin Tarayya Ta Cimma Yarjejeniya Da Kungiyar Malaman Jami’oi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Amurka Ta Baiwa Najeriya Wasu Muhimman Kayan Yaki Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Trump Yayi Kira Ga ‘Yan Ƙasar Iran Su Ci Gaba Da Zanga Zanga Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Syria: Mutane Sun Yi Zanga Zanga Domin Nuna Rashin Amincewa Da Korar Kurdawa A Birnin Aleppo Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Muna Kira Ga Kasashen Duniya Su Sa Baki Don A Saki Mohamed Bazoum
Published: November 27, 2025 at 11:05 PM | By: Yusuf Aliyu Harande

A Jamhuriyar Nijar ‘yayan hambararren shugaban kasa Mohamed Bazoum sun bayyana damuwa dangane da yadda ake ci gaba da tsare mahaifansu sama da shekaru 2 bayan kifar da shi daga karaga.
A cewarsu dukkan abubuwan da a ke zargin bayansu da shi ba su da tushe saboda haka su ke kiran kasashen duniya su dubi wannan batu.
A yayin da shugaba Mohamed Bazoum da mai dakinsa Hadiza Bazoum ke cika watanni 28 a tsare ne ‘yayansu suka fitar da sanarwar hadin guiwa domin tada duniya daga barci dangane da halin da mahaifansu ke ciki Wanda kuma su kansu ke shafar ra’ayinsu inji su. Hinda Mohamed Bazoum na daga cikin ‘yayan hambararren shugaban kasar ta Nijar.
Mohamed Bazoum wanda ke tsare a fadar shugaban kasa na fuskantar zarge zargen da hukumomi suka ayyana a matsayin cin amanar kasa. sai dai ‘yayansa na ganin Babu wasu hujjojin da ke gaskata laifikan da ake zarginsa da su.
Kawo yanzu ba wata sanarwar gwamnati a game da wannan batun.
A Watan yunin 2024 kotun shara’ar manyan Jami’an gwamnatin Nijar ta cire wa Mohamed Bazoum rigar kariya amma har zuwa wannan lokaci ba a taba gurfanar da shi gabn alkali ba domin yi masa shari’a.
A baya kotun ECOWAS da kungiyoyin kasa da kasa har ma da hukumar Majalisar Dinkin Duniya mai kula da kare hakkin dan adam sun bukaci gwamnatin mulkin sojan Nijar ta sallame shi sai dai wadanan kiraye kiraye ba su samu karbuwa ba.
SANARWAR YAYAN BAZOUM (1)
Afrika

Post navigation

Previous Post: An Bude Gasar Kwallon Kafa Ta Mata A Najeriya NWFL 2025
Next Post: Mutane Da Yawa Ke Mutuwa A Dalilin Shan Magani Ba Bisa Ka’ida Ba

Karin Labarai Masu Alaka

Kungiyar ECOWAS Ta Koka Game Da Yawan Juyin Mulki A Kasashen Afirka Afrika
Kasar Gambiya Ta Gayawa Kotun MDD Shirin Myanmar Akan Musulmai Afrika
Harin Makami Mai Linzami Da Rasha Ta Kai Yayi Barna Sosai A Ukraine Afrika
Babban Hafsan Sojan Libya Ya Mutu A Wani Hatsarin Jirgin Saman Turkiyya Afrika
Kasar Habasha Ta Cimma Matsaya Da Masu Binta Bashi Afrika
Sanyin Hunturu Yayi Ajalin ‘Yan Cirani A Morocco Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Najeriya Ta Dauki Hayan Amurkawa Don Kyautata Alaka Da Trump Game Da Kisan Kiristoci
  • Gwamnatin Tarayya Ta Cimma Yarjejeniya Da Kungiyar Malaman Jami’oi
  • Kabiru Vice: Najeriya Zata Iya Nasara A Kan Moroko AFCON 2025.
  • Motar Yashi Ta Kashe Mutane Shida A Wani Coci Dake Legas
  • An Kaddamar Da Rijistar Zamani Ta Zamowa Mamba A Jam’iyar APC

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • Amurka Ta Bada Tabbacin Baiwa Ukraine Tsaron Na Shekaru 15 Amurka
  • Ansamu Girgizar Kasa A Kasar Taiwan Labarai
  • Kwankwaso: Gwamnatin Kano Tamuce Baki Daya, Tafiya APC Allah Ya Raka Taki Gona! Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Kungiyar Kiristoci Ta Wanke Gwamnan Bauchi Daga Zargin Ta’addanci Labarai
  • Hukumar Ƴan Sanda Ta Musanta Zargin Kashe Ɗan Achaba a Gombe Tsaro
  • Eziekel Gomos Ya Zamo Babban Daraktan Sakatariyar Zauren Gwamnonin Arewa Najeriya
  • Rundunan  ‘Yan Sandan Jihar Bauchi, Ta Miƙa Miyagun Ƙwayoyi Da Ta Kama Wa NDLEA. Labarai
  • Kotun Kasar Rasha Ta Daure Dan Kasar Belarus Shekarar 22 A Kurkuku Labarai
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.