Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Kotu Ta Bada Belin Nasiru El Rufai Afrika
  • Najeriya Da Jamus Sun Kulla Yarjejeniyar Zuba Jari Afrika
  • Zaben Fidda Gwani Ya Gudana Lafiya A Jihar Gombe Afrika
  • Sojin Najeriya Da Amurka Sun Hallaka Jagoran ISIS Afrika
  • Hukumar ‘Yan Sanda Tayi Yarjejeniya Da ‘Yan Takara A Gombe Afrika

Amurkawa Sun Nuna Bacin Rai Saboda Yawaita Kashe ‘Yan Kasar
Published: January 27, 2026 at 9:58 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Madugun aikin korar bakin haure a gwamnatin shugaba Donald Trump, ranar talata ya gana da gwamnan jihar Minnesota Tim Watz, bayan da ya karbi jagorancin Gudanar da shirin korar ‘yan gudun hijira ko bakin haure na babu kama hannun yaro a birnin Minneapolis, yayin da fadar White House take kokarin sassauta irin bacin rai da Amurkawa a duk fadin kasar suka nuna, bayan da jami’an hukumar shige da fice suka kashe ba Amurke na biyu cikin watan nan a birnin na Minneapolis.

A cikin wata sanarwa da tashar talabijin din CNN ta ruwaito, gwamna Waltz yace jihar ta bayyana wa Homan muradun ta da suka hada da gudanar da bincike babu son rai kan kisan mutanen nan biyu, da kuma rage jami’an aikin shige da fice su dubu uku da gwamnatin tarayya ta tura zuwa birnin na Minneapolis. Sanarwar tace, Homan da Waltz sun amince zasu ci gaba da aiki tare domin cimma wannan buri.

Matakin gwamnatin Trump na tura Homan ya maye babban jami’in aiki shige da fice Gregory Bovino, ya biyo bayan damuwar da mukarraban shugaban na Amurka suka nuna cewa kashe Alex Pretti dan shekaru 37 da haifuwa yana iya gurgunta shirin gwamnatinsa kan bakin haure.

Amurka

Post navigation

Previous Post: Kasar Spain Zata Bada Diyya Ga Iyalen Wadanda Da Suka Rasu A Hatsarin Jirgin Kasa
Next Post: Gwamnatin Tinubu Zata Gyara Hanyar Akwanga Zuwa Jos

Karin Labarai Masu Alaka

Shugaban Kasar Brazil: Yakamata Amurka Ta Gurfanar Da Shugaban Venezuela A Kotu Afrika
Farashin Mai Yana Cigaba Da Karuwa Afrika
Shugaban Amurka Yayi Watsi Da Tattaunawar Kawo Karshen Yaki Da Iran Afrika
Wani Jirgin Sama Ya Karya Dokar Hana Zirga Zirga Amurka
Kasar Canada Ta Amince A Shigar Da Motoci Kirar Kasar China Kasar Amurka
Amurka Ta Yi Juyin Mulki A Kasar Venezuela Amurka

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Kotu Ta Bada Belin Nasiru El Rufai
  • Najeriya Da Jamus Sun Kulla Yarjejeniyar Zuba Jari
  • Zaben Fidda Gwani Ya Gudana Lafiya A Jihar Gombe
  • Sojin Najeriya Da Amurka Sun Hallaka Jagoran ISIS
  • Hukumar ‘Yan Sanda Tayi Yarjejeniya Da ‘Yan Takara A Gombe

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Gwamnan Jihar Filato Na Shirin Komawa APC Siyasa
  • Kasashen Cambvodia Da Thailand Sun Kulla Yarjejeniyar Tsagaita Wuta Tsaro
  • An Kai Hari Babbar Tashar Iskar Gas A Iran Afrika
  • Amurka Ta Bada Tabbacin Baiwa Ukraine Tsaron Na Shekaru 15 Amurka
  • Indiya Da Brazil Sun Kulla Yarjejeniyar Cinikayya Afrika
  • An Canza Shugabannin Hukumar Hakar Ma’adanai A Congo Labarai
  • An Gudanar Da Idin Karamar Sallah A Birnin Niamey Labarai
  • An Kafa Majalisar Kotun Sulhu Ta Kano Labarai
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.