Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • PDP Ta Tsayar da Goodluck Jonathan Takarar Shugaban Kasa Afrika
  • Hawan Gidan Gwamnati A Jihar Gombe Afrika
  • Hawan Babbar Sallah A Masarautar Kaltungo Dake Jihar Gombe Afrika
  • Sarkin Gombe Ya Yabi Nasarorin Inuwa Yahaya A Fannonin Tsaro Da Raya Kasa Afrika
  • Tinubu Ya Jaddada Aniyar Rage Tsadar Rayuwa Da Samar da Ayyukan Yi Afrika

Mutane Da Yawa Ke Mutuwa A Dalilin Shan Magani Ba Bisa Ka’ida Ba
Published: November 27, 2025 at 11:15 PM | By: Yusuf Aliyu Harande | Updated: December 18, 2025

Hukumar lafiya ta duniya ta ayyana bijirewar cututtuka ga maganguna a matsayin babban al’amari dake kawo cikas da barazana a bangaren kiwon lafiyar jama’ah.
Najeriya dai ta kasance kasa ta 19 wajen rasa rayuka a cikin kasashe 204, kuma ana danganta mutuwar mutum dubu dari biyu da sittin da uku da dari hudu da matsalar Anti Microbial Resistance (AMR).
Dr. Muslim Bello Katagum yace AMR na nufin yadda cututtuka basa jin magani sakamakon shansu da ake yi ba bisa ka’ida ba.
Ganin yadda wannan matsala ke kara ta’azzara a duniya yasa Danida Alumni wato Dalibai da suka samu horo daga Danish International Development Agency, wato hukumar dake kula da cigaban kasashe ta kasar Denmark suka gudanar da taron a Abuja, domin watar da kan masu ruwa da tsaki da suka hada da NAFDAC, Standard Organisation Of Nigeria (SON), manoma, da sauransu domin tattauna hanyoyin wayar da kai don shawo kan matsalar AMR.
Sakataren Danida Alumni Nasiru Usman yace sun lura wannan matsala na daga cikin abubuwan dake damun Najeriya shiya suka shirya taron domin domin gwamnati ta kara maida hankali da sa ido kan lamarin.
Wakili daga Gonar Medogi Idris Usman Ibrahim yace taron ya kara fahimtar dasu yadda abun yake, inda ya kara da cewa a yanzu zasu maida hankali wajen bin ka’idar magani ga dabbobi da shuka.
Khadija Muhammad dake aiki da ma’aikatar kula da muhalli a sashen hana gurbacewar muhalli da kuma kula da lafiyar muhalli, jan hankali tayi wajen kula da tsaftar muhalli don gujewa cututtuka.
Matsalar AMR dai na daga cikin manyan matsaloli da hukumar lafiya ta duniya (WHO) tafi maida hankali akai a yanzu,ganin yadda matsalar ke haifar da salwantar rayuka da yaduwar cututtuka.
https://gtahausa.com/wp-content/uploads/2025/11/AMR-GLOBAL-THREAT.mp3
Kiwon Lafiya, Najeriya

Post navigation

Previous Post: Muna Kira Ga Kasashen Duniya Su Sa Baki Don A Saki Mohamed Bazoum
Next Post: Sunayen Jakadu: Kungiyar CISLAC Ta Nemi A Janye Sunan Mr. Ayodele Oke

Karin Labarai Masu Alaka

Shugaban Kasar Najeriya Ya Gabatar Da Kudi Fiye Da Naira Triliyan 58 A Matsayin Kasafin 2026 Najeriya
Taron Masu Mu’amala Da Kafar Facebook A Kano Afrika
Magoya Bayan Tijjaniyya Zasu Kauracewa Zabe Saboda Kama Sheikh Sani Khalifa Afrika
Tinubu, Akpabio da Ministoci 9 Zasu Tafi Ƙasar Birtaniya Afrika
Ganduje Ya Nisanta Kansa Da Batan Dadiyata Labarai
Hukumar Hisbah Ta Kona Barasar Dubban Nairori A Katsina Labarai

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • PDP Ta Tsayar da Goodluck Jonathan Takarar Shugaban Kasa
  • Hawan Gidan Gwamnati A Jihar Gombe
  • Hawan Babbar Sallah A Masarautar Kaltungo Dake Jihar Gombe
  • Sarkin Gombe Ya Yabi Nasarorin Inuwa Yahaya A Fannonin Tsaro Da Raya Kasa
  • Tinubu Ya Jaddada Aniyar Rage Tsadar Rayuwa Da Samar da Ayyukan Yi

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Shugaba Tinubu Ya Nada Shugaban NAHCON Labarai
  • An Gudanar Da Idin Karamar Sallah A Birnin Niamey Labarai
  • Kudin Man Fetur Ya Karu Da Kashi 10 Cikin 100 Afrika
  • Tinubu Ya Yi Allah Wadai Da Kashe-kashen Jos Da Kaduna Afrika
  • Sojoji Sun Fatattaki ‘Yan Ta’adda A Borno Tsaro
  • Umar Ya Lashe Kyautar Gwarzon ‘Dan-Wasa Na 2025 Wasanni
  • Zamfara: Sai Mun Hada Kai Don Kawo Karshen Ta’addanci Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Ranar Lahadi Anyi Zaben Shugaban Kasa A Congo Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.