Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Sojojin Najeriya Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda Da Dama Afrika
  • An Sace Wani Shugaban Karamar Hukuma A Jihar Zamfara Afrika
  • Aikin Tsaftar Muhalli Na Wata-Wata Ya Samu Gagarumar Nasara A Gombe Afrika
  • Tinubu Ya Sake Fasalin Rundunar Sojin Ƙasa Domin Inganta Tsaro Afrika
  • Gombe Ta Haɗa Kai Da UNICEF Don Kare Yara Daga Tamowa Tun Kafin Haihuwa Afrika

Mutane Da Yawa Ke Mutuwa A Dalilin Shan Magani Ba Bisa Ka’ida Ba
Published: November 27, 2025 at 11:15 PM | By: Yusuf Aliyu Harande | Updated: December 18, 2025

Hukumar lafiya ta duniya ta ayyana bijirewar cututtuka ga maganguna a matsayin babban al’amari dake kawo cikas da barazana a bangaren kiwon lafiyar jama’ah.
Najeriya dai ta kasance kasa ta 19 wajen rasa rayuka a cikin kasashe 204, kuma ana danganta mutuwar mutum dubu dari biyu da sittin da uku da dari hudu da matsalar Anti Microbial Resistance (AMR).
Dr. Muslim Bello Katagum yace AMR na nufin yadda cututtuka basa jin magani sakamakon shansu da ake yi ba bisa ka’ida ba.
Ganin yadda wannan matsala ke kara ta’azzara a duniya yasa Danida Alumni wato Dalibai da suka samu horo daga Danish International Development Agency, wato hukumar dake kula da cigaban kasashe ta kasar Denmark suka gudanar da taron a Abuja, domin watar da kan masu ruwa da tsaki da suka hada da NAFDAC, Standard Organisation Of Nigeria (SON), manoma, da sauransu domin tattauna hanyoyin wayar da kai don shawo kan matsalar AMR.
Sakataren Danida Alumni Nasiru Usman yace sun lura wannan matsala na daga cikin abubuwan dake damun Najeriya shiya suka shirya taron domin domin gwamnati ta kara maida hankali da sa ido kan lamarin.
Wakili daga Gonar Medogi Idris Usman Ibrahim yace taron ya kara fahimtar dasu yadda abun yake, inda ya kara da cewa a yanzu zasu maida hankali wajen bin ka’idar magani ga dabbobi da shuka.
Khadija Muhammad dake aiki da ma’aikatar kula da muhalli a sashen hana gurbacewar muhalli da kuma kula da lafiyar muhalli, jan hankali tayi wajen kula da tsaftar muhalli don gujewa cututtuka.
Matsalar AMR dai na daga cikin manyan matsaloli da hukumar lafiya ta duniya (WHO) tafi maida hankali akai a yanzu,ganin yadda matsalar ke haifar da salwantar rayuka da yaduwar cututtuka.
https://gtahausa.com/wp-content/uploads/2025/11/AMR-GLOBAL-THREAT.mp3
Kiwon Lafiya, Najeriya

Post navigation

Previous Post: Muna Kira Ga Kasashen Duniya Su Sa Baki Don A Saki Mohamed Bazoum
Next Post: Sunayen Jakadu: Kungiyar CISLAC Ta Nemi A Janye Sunan Mr. Ayodele Oke

Karin Labarai Masu Alaka

PDP Ta Tsayar da Goodluck Jonathan Takarar Shugaban Kasa Afrika
Hukumar EFCC Ta Kama Dan Kasuwa A Kamaru Afrika
Gwamnatin Tarayya Ta Cire Sharadin Rubuta UTME Ga Masu Neman Shiga Kwalejojin Ilimi Afrika
Sanata Goje Yayi Watsi Da Fidda ‘Yan Takarar APC A Gombe Afrika
Yohanna YD Buru: Makon Haɗin Kan Addinai Ya Ƙarfafa Ilimin Zaman Lafiya A Najeriya Labarai
Jam’iyar SDP Tana Gudanar Da Babban Taro A Bauchi Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Sojojin Najeriya Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda Da Dama
  • An Sace Wani Shugaban Karamar Hukuma A Jihar Zamfara
  • Aikin Tsaftar Muhalli Na Wata-Wata Ya Samu Gagarumar Nasara A Gombe
  • Tinubu Ya Sake Fasalin Rundunar Sojin Ƙasa Domin Inganta Tsaro
  • Gombe Ta Haɗa Kai Da UNICEF Don Kare Yara Daga Tamowa Tun Kafin Haihuwa

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Gwamnatin Najeriya Ta Karyata Raɗe-Raɗin Canza Sunan Kasar Da Soke Shari’a A Arewa Afrika
  • Sarkin Kagarko Ya Rasu Yana Da Shekaru 110 Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Aminu Tambuwal Ya Fice Daga PDP Ya Koma ADC Afrika
  • ‘Yan Sandan Bauchi Sun Kama Mutum Biyu Kan Zargin Fashi da Makami A Gadau Afrika
  • An Zargi Kasar Eritrea Da Cin Zarafin Sojojin Habasha Afrika
  • Yakin Gabas Ta Tsakiya Ya Haifar Da Tsadar Taki Da Mai Ga Manoma Labarai
  • Ankara Kai Wani Harin Bom Birnin Maiduguri Afrika
  • Najeriya: Ba Don Leken Asiri Muka Tura Jirgin Yakin Mu Ba Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.