Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • ’Yan Sandan Gombe Sun Kama Wanda Ake Zargi Da Garkuwa Da Mutane Da Dillalin Miyagun Ƙwayoyi Afrika
  • Gwamnan Gombe Ya Rantsar Da Sabbin Manyan Sakatarori 19 Afrika
  • CBCN Ta Ce Za Ta Ci Gaba Da Goyon Bayan Tinubu A Zaɓen 2027 Afrika
  • Gwamna Bala Mohammed Ya Miƙa Ta’aziyyar Rasuwar Abdullahi Sule Madaki Afrika
  • Al’ummar Wajari Sun Amfana Da Gyaran Cibiyar Kiwon Lafiya Matakin Farko Afrika

Shugaban Gwamnonin Arewa Ya Bukaci Musulmi Su Rungumi Tausayi Da Ƙaunar Juna
Published: May 27, 2026 at 6:37 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Muhammadu Inuwa Yahaya ya taya al’ummar Musulmi murnar bikin Eid el-Kabir na bana, inda ya yi kira ga muminai da su rungumi dabi’un sadaukarwa, ƙauna, haɗin kai da biyayya kamar yadda Annabi Ibrahim (AS) ya nuna kuma Annabi Muhammad (SAW) ya tabbatar.

A cikin saƙon taya murna da ya fitar domin bikin Sallah, gwamnan ya bayyana Eid el-Kabir a matsayin lokaci na sadaukarwa, rabon arziki da tausayi, yana mai kira ga Musulmi da su ci gaba da tabbatar da zaman lafiya da zaman tare cikin jituwa a cikin al’umma.

Gwamna Inuwa Yahaya ya jaddada muhimmancin ci gaba da yin addu’o’i domin zaman lafiya, ci gaba da bunƙasar tattalin arziki mai ɗorewa a Jihar Gombe da Najeriya baki ɗaya, musamman duba da ƙalubalen tattalin arziki da matsalolin tsaro da ƙasar ke fuskanta.

“Jihar Gombe na cikin zaman lafiya, kwanciyar hankali da ci gaba, kuma hakan ya samo asali ne daga ruhin zaman lafiya, haɗin kai duk da bambance-bambance da kuma haƙuri da aka daɗe ana gina wa a tsakanin al’ummarmu. Don haka ina kira gare mu da mu ci gaba da kiyaye wannan kyakkyawan yanayi,” in ji gwamnan.

Gwamnan, wanda kuma shi ne shugaban Ƙungiyar Gwamnonin Jihohin Arewa, ya bayyana cewa bikin Eid na bana ya zo ne daidai da fara harkokin siyasa gabanin babban zaɓen shekarar 2027, inda ya yi gargadin kada siyasa ta mamaye darussa da muhimmancin ibadar da ke cikin wannan biki.

A cewarsa, wannan lokaci ya kamata ya zama tunatarwa kan tausayi, sadaukarwa, biyayya ga Allah Maɗaukakin Sarki da kuma ƙaunar juna, maimakon rarrabuwar kai da gasa ta siyasa mara kyau.

Ya kuma bayyana godiyarsa ga sarakunan gargajiya, shugabannin addini da na al’umma, tare da daukacin jama’ar Jihar Gombe bisa ci gaba da ba gwamnatinsa haɗin kai da goyon baya.

Gwamnan ya sake jaddada ƙudirin gwamnatinsa na ci gaba da aiwatar da manufofi, shirye-shirye da ayyukan ci gaba da za su bunƙasa tattalin arziki da rayuwar al’ummar jihar.

Haka kuma, ya buƙaci mazauna jihar da su kasance masu lura da tsaro tare da kai rahoton duk wani abu da ake zargi da zai iya barazana ga zaman lafiya da kwanciyar hankalin da ake morewa a jihar.

“Gwamnati ba za ta yi watsi da babban nauyin da ke kanta na kare rayuka da dukiyoyin jama’a ba. Za mu ci gaba da tallafawa jami’an tsaro domin tabbatar da dorewar zaman lafiya da tsaro a faɗin jiharmu,” in ji shi.

Dangane da damina kuwa, Gwamna Inuwa Yahaya ya yi kira ga jama’a da su yi addu’ar samun wadataccen ruwan sama da albarkar noma, tare da ɗaukar matakan kariya daga ambaliya.

Ya shawarci jama’a da su tsaftace muhallansu, su buɗe magudanan ruwa tare da kauce wa zama a wuraren da ambaliya ke yawan faruwa domin rage illolin ambaliyar ruwa a lokacin damina.

A ƙarshe, gwamnan ya yi addu’ar Allah Ya sa a gudanar da bikin Eid cikin zaman lafiya, kwanciyar hankali da albarkar Allah ga al’ummar Jihar Gombe da Najeriya baki ɗaya.

Afrika, Labarai, Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu, Najeriya, Nishadi

Post navigation

Previous Post: Hamma Saleh Ya Yi Fatali da Bai Wa Pantami Takarar Gwamna a PDP
Next Post: Shugabannin Kiristoci Sun Halarci Filin Idi A Kaduna Domin Nuna Haɗin Kai

Karin Labarai Masu Alaka

ECOWAS Ta Saka Dokar Ta Baci A Afrika Ta Yamma Afrika
Kotu A Najeriya Ta Kame Mutane Bisa Zargin Ta’addaci Afrika
Bola Ahmed Tinubu Ya Soke Bashin Da Gwamnati Take Bin NNPC Najeriya
Hari Da Jirgi Marar Matuki Ya Kashe Mutane Da Dama A Darfur Labarai
Gwamnan Gombe Ya Amince Da Naɗin Manyan Sakatarori 19 Afrika
Akwai Alamar Shawarwari Tsakanin Amurka Da Turai Zai Kawo Karshen Yakin Rasha Amurka

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • ’Yan Sandan Gombe Sun Kama Wanda Ake Zargi Da Garkuwa Da Mutane Da Dillalin Miyagun Ƙwayoyi
  • Gwamnan Gombe Ya Rantsar Da Sabbin Manyan Sakatarori 19
  • CBCN Ta Ce Za Ta Ci Gaba Da Goyon Bayan Tinubu A Zaɓen 2027
  • Gwamna Bala Mohammed Ya Miƙa Ta’aziyyar Rasuwar Abdullahi Sule Madaki
  • Al’ummar Wajari Sun Amfana Da Gyaran Cibiyar Kiwon Lafiya Matakin Farko

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Na Duke Tsohon Ciniki Shirye-Shirye
  • Makokin Ashura: An Gudanar Da Taron Tunawa Da Aliyul Asghar A Gombe Afrika
  • Meyasa Israela Take Hana Kaiwa Gaza Kayan Tallafi Afrika
  • Likitoci Masu Neman Kwarewa Zasu Shiga Yakin Aiki Afrika
  • Akwai Doka Mai Tsanani Wajen Mallakar Bindiga A Kasashen Yammacin Turai Labarai
  • Bahrain Ta Gabatar Da Kudurin Sulhu Ga MDD Afrika
  • Rasha Takai Hari Ukraine Da Jirgi Marar Matuki Afrika
  • Kurdawa Sun Gargadi ‘Yan Uwansu Game Da Alaka Da Amurka Wajen Yakar Iran Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.