Shugaban Hukumar Alhazai ta Najeriya wato (NAHCON), Ambasada Isma’il Abba Yusuf, ya yaba wa tawagar ‘yan jaridun Najeriya da ke gudanar da aikin yada labarai a Saudiyya bisa yadda suka gudanar da rahotannin Hajjin shekarar 2026 cikin kwarewa da jajircewa.
Ambasada Yusuf ya bayyana hakan ne a yayin wata ganawa da ‘yan jaridar a Ofishin NAHCON dake birnin Makkah ranar Lahadi, inda ya ce ya gamsu matuka da inganci da kuma sahihancin rahotannin da suka rika aikawa daga wuraren ibadar Hajji.
“Na ga ya dace in gana da ku domin in isar da godiya ta kai tsaye. Hakika na yi matukar farin ciki da irin aikin da kuka yi da kuma yadda kuka nuna kwarewa da jajircewa duk da matsin lambar da ke tattare da aikin,” in ji shi.
Ya ce hukumar na shirin aiwatar da wasu gyare-gyare da sauye-sauye domin kara inganta ayyukan Hajji a nan gaba, tare da samar da yanayi mafi dacewa ga ‘yan jarida domin gudanar da aikinsu cikin sauki.
A cewarsa, duk da karancin albarkatun da hukumar ke da su wajen sakawa masu yada labarai, NAHCON na da cikakken masaniya kan irin wahalhalun da suke fuskanta yayin gudanar da aikinsu.
“Mun san irin hatsarori da wahalhalun da aikin ke tattare da su. Mun san lokutan da kuke yin tafiya mai nisa domin neman labari. Saboda haka muna matukar godiya da irin hakurin da kuka nuna da kuma yadda kuka gudanar da aikinku cikin kwarewa,” inji shi
Shi ma da yake jawabi, Kwamishinan NAHCON mai kula da Ma’aikata, Bincike, Watsa Labarai da Ayyukan Laburare, Farfesa Abubakar Yagawal, ya yabawa ‘yan jaridar bisa irin gudunmawar da suka bayar wajen yada bayanai kan ayyukan Hajjin bana.
Ya ce baya ga rawar da suka taka wajen isar da labarai ga al’umma, sun kuma kasance masu bayar da goyon baya ga hukumar a lokuta daban-daban yayin gudanar da ayyukan Hajji.
“Muna matukar godiya da irin kokarin da kuka yi wajen yada ayyukan Hajji da kuma tafiyar da harkokin aikin Hajjin bana. Yawancin rahotannin da aka fitar a wannan shekara sun kasance masu inganci, saboda haka muna mika godiyarmu gare ku baki daya,” in ji Yagawal.
Ya kara da cewa hadin kai tsakanin NAHCON da kafafen yada labarai na da matukar muhimmanci wajen tabbatar da sahihan bayanai sun isa ga alhazai da kuma ‘yan Najeriya baki daya.


