Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Dakarun Sojin Najeriya Sun Kashe Yan Kungiyar Lakurawa Afrika
  • Shugaba Tinubu Ya Yabawa Dakarun Tsaro Bisa Ceto Matar Marigayi Janar Rabe Afrika
  • Sabuwar Shekarar Musulunci 1448: Kiristoci Sun Yi Murna, Sunyi Kiran Samar Da Hutu Ga Shekarar Musulunci Afrika
  • Sabuwar Shekarar Musulunci: Shugaban Gwamnonin Arewa Ya Yi Kira Da A Yawaita Addu’o’i Da Haɗin Kai Afrika
  • EU Ta Yi Maraba Da Yarjejeniyar Amurka Da Iran Afrika

Rashin Hanya da Asibiti Ya Jawo Asarar Rayuka A Jihar Gombe – Sarkin Gargajiya
Published: June 18, 2026 at 7:23 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Sarkin Jaurowal dake Masarautar Pindiga, Karamar Hukumar Akko ta Jihar Gombe, Comrade Ambassador Ibrahim Mu’azu Hassan, ya roƙi gwamnatoci a dukkan matakai su samar da muhimman kayan more rayuwa ga al’ummar da ke ƙarƙashinsa.

Yayin da yake Tattaunawa da Wakilin Amurka Ke Magana a jihar Gombe, sarkin ya roƙi shugabannin siyasa, masu hannu da shuni, da kuma ƙungiyoyi masu zaman kansu su tallafawa yankin ta hanyar sauƙaƙa samar da Hanyoyi, Cibiyoyin lafiya, da Makarantun ilimi.

Mu’azu Hassan ya bayyana damuwarsa kan halin da ababen more rayuwa ke ciki a yankin, musamman hanyoyi, wanda ya ce ya haddasa mutuwar akalla mata 5 da ba su samu damar samun magani a kan lokaci ba yayin da ake ɗaukarsu zuwa asibiti.

Ya yi kira ga gwamnatin Gwamna Alhaji Muhammadu Inuwa Yahaya, Sanata Danjuma Goje mai wakiltar Gombe ta Tsakiya, da Dr. Usman Bello Kumo ɗan majalisar tarayya mai wakiltar Akko, Alhaji Abubakar Abdullahi Mai Wanka dan majalisa mai wakiltar Akko ta Yamma dasu shiga tsakani su magance matsalolin da al’ummar yankin ke fuskanta.

Sarkin ya kuma yi ƙorafi kan watsar da aikin gina Makarantar Junior Secondary School ta Jaurowal da aka shirya yinta kuma basuyi ba har yau, inda ya ce ginin ya tsaya shekaru 7 da suka wuce, ya kuma ƙara da cewa mazauna yankin suna fama da matsaloli wajen samun ingantaccen ilimi da lafiya.

Ya kara roƙon gwamnati ta ba yankin kulawa, ta kuma ƙirƙiri “Ward” saboda Jaurowal yana da kauyuka kusan 10, ciki har da Garin Jauro Jibir, Labarfito, Dongoru Karama, Felawa, Bakkiti, Pali, Lafiyawo, da Ardowu,Garin Yabano etc.

Duk da yawan jama’a da gudummawar da suke bayarwa ga karamar hukumar, ya ce al’ummar yankin ba su ci moriyar ayyukan ci gaba da ‘ya’yan dimokuraɗiyya ba har yanzu.

Mu’azu Hassan ya roƙi hukumomi masu dacewa su ba da fifiko ga bukatun yankin, su inganta rayuwar mazauna yankin ta hanyar samar da ababen more rayuwa da ayyukan cigaban al’umma.

A karshe yana addu’a ga kasar Pindiga Emirates da Garin Jaurowal jihar Gombe da Nigerian baki daya da Allah yabasu zaman lfy da cigaba mai dorewa.

Afrika, Kiwon Lafiya, Labarai, Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu, Najeriya, Sauran Duniya, Siyasa, Tsaro

Post navigation

Previous Post: Dakarun Sojin Najeriya Sun Kashe Yan Kungiyar Lakurawa

Karin Labarai Masu Alaka

Trump Yace Kawayen Amurka A Kungiyar NATO Basa Goyon Bayan Su Afrika
Ana Zargin Tsohon Shugaban Kasar Philippines Da Ta’addaci A Lokacin Mulkinsa Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Masu Luwadi Na Fuskantar Tara Da Daurin Shekaru 20 A Nijar Afrika
Najeriya Zata Kara Mai Da Take Hakowa Afrika
Masoya Kungiyar Kwallon Kafar Morocco Suna Cikin Farin Ciki Bisa Hukuncin Kotu Afrika
Real Madrid: Ta Kori Xabi Alonso Bayan Rashin Nasara A Wasan Kofin Sfaniya Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Rashin Hanya da Asibiti Ya Jawo Asarar Rayuka A Jihar Gombe – Sarkin Gargajiya
  • Dakarun Sojin Najeriya Sun Kashe Yan Kungiyar Lakurawa
  • Shugaba Tinubu Ya Yabawa Dakarun Tsaro Bisa Ceto Matar Marigayi Janar Rabe
  • Sabuwar Shekarar Musulunci 1448: Kiristoci Sun Yi Murna, Sunyi Kiran Samar Da Hutu Ga Shekarar Musulunci
  • Sabuwar Shekarar Musulunci: Shugaban Gwamnonin Arewa Ya Yi Kira Da A Yawaita Addu’o’i Da Haɗin Kai

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Al’ummar Jihar Nasarawa Suna Cecekuce Bisa Tsaida Aliyu Wadada Takarar Gwamna Afrika
  • Kasar Chadi Ta Rufe Iyakar Ta Da Kasar Sudan Afrika
  • NAHCON Ta Kaddamar da Tawagar Malamai Afrika
  • Bincike Yanuna Kasashen Afirka Suna Cikin Mafiya Cin Bashi A Duniya Afrika
  • Babban Bankin Najeriya Ya Rage Kudin Ruwa Da Kashi Daya Cikin Dari Labarai
  • Ana Cigaba Da Bincike Game Da Mutuwar Matar Da Likita Ya Manta Almakashi A Cikinta A Kano Najeriya
  • Jirgin Sojin Saman Najeriya Yayi Hatsari a Jihar Neja Labarai
  • Shugaba Trump Yayi Barazanar Tarwatsa Cibiyar Makamashin Iran Amurka
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.