Gwamnatin jihar Gombe ta fara wani shirin horas da ma’aikatan gwamnati kan ƙwarewar fasahar zamani, a wani mataki na ƙara inganta ayyukan gwamnati ta hanyar amfani da fasahar sadarwa.
Shirin horaswar, wanda Hukumar Fasahar Sadarwa da Tattalin Arziƙin Zamani ta Jihar Gombe (GOSIDEC) ta shirya tare da haɗin gwiwar Hukumar Bunƙasa Fasahar Sadarwa ta Ƙasa (NITDA), na da nufin bai wa ma’aikatan gwamnati ilimi da ƙwarewar da za su taimaka musu su dace da buƙatun aikin gwamnati a zamanin dijital.
Da yake ƙaddamar da shirin, Sakataren Gwamnatin Jihar Gombe, Farfesa Ibrahim Abubakar Njodi, ya ce shirin wani ɓangare ne na manufar gwamnatin Gwamna Muhammadu Inuwa Yahaya ta gina ma’aikata masu ƙwarewa, inganta ayyukan gwamnati da kuma samar da hidima mai nagarta ga al’umma.
Ya bayyana cewa ci gaban fasaha ya sauya yadda ake gudanar da ayyuka da harkokin mulki a duniya, yana mai jaddada cewa ƙwarewar fasahar zamani ta zama wajibi ga kowane ma’aikacin gwamnati.
“Gwamnatoci a faɗin duniya na amfani da fasahar zamani wajen inganta ayyuka, ƙarfafa gaskiya da riƙon amana, tare da gaggauta isar da hidima ga jama’a. Don haka dole ne ma’aikatanmu su mallaki ƙwarewar da za ta ba su damar tafiya da wannan sauyi,” in ji Njodi.
Ya ƙara da cewa haɗin gwiwar GOSIDEC da NITDA ya zo ne a daidai lokacin da ake ƙara amfani da fasaha wajen inganta tafiyar da gwamnati, yana mai tabbatar da cewa gwamnatin jihar za ta ci gaba da ba da fifiko ga bunƙasa ƙwarewar ma’aikata.
A nasa jawabin, Shugaban Ma’aikatan Jihar, Farfesa Mu’azu Shehu, ya bayyana ilimin fasahar zamani a matsayin muhimmin ginshiƙi na inganta aiki da gudanar da gwamnati. Ya ce baya ga haɓaka ƙwarewa, ilimin na taimakawa wajen ƙarfafa kariyar bayanai da magance barazanar hare-haren yanar gizo.
Ya buƙaci mahalarta taron su yi amfani da damar horaswar wajen faɗaɗa iliminsu da kuma amfani da sabbin dabarun fasaha wajen inganta ayyukansu.
Shi ma Jami’in Horaswa na Ofishin Shiyya na NITDA, Injiniya Yakubu Musa, ya ce ƙwarewar fasahar sadarwa ta zama wajibi ga ma’aikatan gwamnati domin su iya tafiya da sauye-sauyen da ke faruwa a duniyar aiki.
A cewarsa, haɗin gwiwar NITDA da GOSIDEC an tsara shi ne domin gina ma’aikata masu ƙwarewar fasaha da za su taimaka wajen ƙarfafa aiwatar da manufofin gwamnati da inganta hidimtawa jama’a.
A sakonsa na fatan alheri, Babban Daraktan Hukumar Inganta Aikin Gwamnati, Dakta Abubakar Hassan, wanda Mataimakiyar Darakta Hauwa Mohammed ta wakilta, ya ce horaswar ta zo a kan lokaci, yana mai bayyana cewa zuba jari wajen haɓaka ƙwarewar fasahar zamani, zuba jari ne a makomar aikin gwamnati.
Tun da farko, Babban Daraktan GOSIDEC, Dakta Al-Amin Barambu, ya bayyana horaswar a matsayin wani muhimmin mataki na ƙoƙarin gwamnatin jihar na bunƙasa sauyin fasahar zamani da gina ma’aikata masu ƙwarewa.
Ya yaba wa NITDA kan haɗin gwiwar da take bayarwa wajen haɓaka ilimin fasahar zamani a Najeriya, yana mai tabbatar da cewa gwamnatin Gwamna Muhammadu Inuwa Yahaya za ta ci gaba da saka hannun jari wajen gina ma’aikatan gwamnati masu ƙwarewa da za su iya gogayya da takwarorinsu a kowane mataki.
Ana sa ran shirin horaswar zai taimaka wajen inganta ƙwarewar ma’aikatan gwamnati, haɓaka ingancin ayyuka da kuma hanzarta sauya Jihar Gombe zuwa gwamnati mai amfani da fasahar zamani.


