Za a fara gudanar da jana’izar Jagoran Ƙolin Iran da aka ce ya rasu sakamakon hare-haren da Amurka da Isra’ila suka kai a farkon yaƙin.
Za a fara bukukuwan jana’izar ne a ƙarshen mako a Tehran, sannan a ci gaba da jerin gwanon jana’izar a mako mai zuwa a biranen Qom da Mashhad, tare da wasu bukukuwa a ƙasar Iraki.
Limamin sallar Juma’a na birnin Qom, Ayatollah Mohammad Saidi, ya shaida wa kafafen yaɗa labaran gwamnati cewa dimbin mutanen da za su halarci jana’izar zai zama wata alama ta goyon bayan Jamhuriyar Musulunci.
Rahotanni sun ce gwamnatin Iran na shirin tattara miliyoyin magoya baya daga sassa daban-daban na ƙasar, tare da samar musu da sufuri, masauki da abinci, domin nuna ƙarfin gwamnati bayan yaƙin da ta bayyana a matsayin babban ƙalubale ga wanzuwarta.
Haka kuma, rahotanni sun ce mutuwar jagoran da kuma maye gurbinsa da ɗansa, Mojtaba Khamenei, a matsayin Jagoran Ƙoli na uku na Jamhuriyar Musulunci, na daga cikin manyan sauye-sauyen siyasa a tarihin ƙasar cikin shekaru 47 da suka gabata.
An kuma ruwaito cewa Mojtaba ya samu munanan raunuka a harin da ya kashe mahaifinsa, kuma tun bayan fara yaƙin ba a sake ganinsa a bainar jama’a ba.
Sai dai wasu masana na cewa, duk da ƙoƙarin gwamnati na nuna haɗin kai, akwai alamun cewa wasu daga cikin al’ummar Iran na ci gaba da nuna rashin gamsuwa da halin matsin tattalin arziki, takunkuman ƙasashen waje da kuma salon mulkin ƙasar.
Wata mazauniyar Tehran mai suna Samira, mai shekaru 35, ta ce ita da iyalanta ba sa shirin halartar jana’izar, kuma sun bar birnin domin kauce wa cunkoso da tsauraran matakan tsaro.


