Mai Martaba Sarkin Gombe, Alhaji Abubakar Shehu Abubakar na III, ya yi kira ga sarakunan gargajiya da su ƙara haɗa kai domin inganta haɗin kan ƙasa, zaman lafiya, tsaro da kuma kare al’adun gargajiya.
Sarkin ya yi wannan kira ne yayin wata ziyarar girmamawa da ya kai wa Mai Martaba Sarkin Zazzau, Malam Ahmed Nuhu Bamalli, a fadarsa da ke Zariya.
Ya bayyana cewa ƙarfafa hulɗa da haɗin gwiwa tsakanin masarautun gargajiya na da matuƙar muhimmanci wajen magance ƙalubalen da ke barazana ga haɗin kan ƙasa da kuma ci gaban al’ummomi.

Ya ce ziyarar ta kasance ne domin ƙara ƙarfafa kyakkyawar alaƙar da ta daɗe tsakanin Masarautun Gombe da Zazzau.
“Ba wannan ne karon farko da muka haɗu ba. Manufar wannan ziyara ita ce ƙarfafa ‘yan’uwantaka, haɗin kai da kuma zumunci tsakanin masarautunmu,” in ji Sarkin Gombe.
Sarkin ya ƙara da cewa ci gaba da tattaunawa da shawarwari tsakanin sarakunan gargajiya zai taimaka wajen bunƙasa zaman lafiya, inganta tsaro, kare ɗimbin al’adun Najeriya da kuma ƙarfafa haɗin kan al’umma.
Haka kuma, ya yabawa jagorancin Sarkin Zazzau, yana mai cewa sarakunan gargajiya na taka muhimmiyar rawa wajen tallafa wa gwamnati wajen samar da ci gaba mai ɗorewa da zaman lafiya tsakanin al’umma.
Da yake mayar da martani, Mai Martaba Sarkin Zazzau, Malam Ahmed Nuhu Bamalli, ya ce ziyarar ta sake tabbatar da ɗorewar alaƙar da ke tsakanin masarautun gargajiyar Najeriya tare da nuna ƙudurin su na haɗa kan ƙasa.
Ya bayyana cewa dangantakar tarihi tsakanin Masarautun Zazzau da Gombe ta samo asali tun daga ƙarni na 19, a lokacin juyin juya halin Musulunci na Shehu Usmanu Ɗanfodiyo, wanda ya bunƙasa shugabanci nagari, ilimi da zaman lafiya a Arewacin Najeriya.
Sarkin Zazzau ya kuma yi kira ga ‘yan Najeriya da su rungumi haɗin kai da haƙuri da juna, yana mai jaddada cewa sarakunan gargajiya za su ci gaba da jajircewa wajen inganta zaman lafiya, ilimi, ci gaban al’umma da haɗin kan ƙasa.

