Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Sojojin Najeriya Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda Da Dama Afrika
  • An Sace Wani Shugaban Karamar Hukuma A Jihar Zamfara Afrika
  • Aikin Tsaftar Muhalli Na Wata-Wata Ya Samu Gagarumar Nasara A Gombe Afrika
  • Tinubu Ya Sake Fasalin Rundunar Sojin Ƙasa Domin Inganta Tsaro Afrika
  • Gombe Ta Haɗa Kai Da UNICEF Don Kare Yara Daga Tamowa Tun Kafin Haihuwa Afrika

Sarakunan Gombe Da Zazzau Sun Yi Kira Ga ‘Yan Najeriya Su Rungumi Haɗin Kai Da Zaman Lafiya
Published: July 8, 2026 at 9:14 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Mai Martaba Sarkin Gombe, Alhaji Abubakar Shehu Abubakar na III, ya yi kira ga sarakunan gargajiya da su ƙara haɗa kai domin inganta haɗin kan ƙasa, zaman lafiya, tsaro da kuma kare al’adun gargajiya.

Sarkin ya yi wannan kira ne yayin wata ziyarar girmamawa da ya kai wa Mai Martaba Sarkin Zazzau, Malam Ahmed Nuhu Bamalli, a fadarsa da ke Zariya.

Ya bayyana cewa ƙarfafa hulɗa da haɗin gwiwa tsakanin masarautun gargajiya na da matuƙar muhimmanci wajen magance ƙalubalen da ke barazana ga haɗin kan ƙasa da kuma ci gaban al’ummomi.


Ya ce ziyarar ta kasance ne domin ƙara ƙarfafa kyakkyawar alaƙar da ta daɗe tsakanin Masarautun Gombe da Zazzau.

“Ba wannan ne karon farko da muka haɗu ba. Manufar wannan ziyara ita ce ƙarfafa ‘yan’uwantaka, haɗin kai da kuma zumunci tsakanin masarautunmu,” in ji Sarkin Gombe.
Sarkin ya ƙara da cewa ci gaba da tattaunawa da shawarwari tsakanin sarakunan gargajiya zai taimaka wajen bunƙasa zaman lafiya, inganta tsaro, kare ɗimbin al’adun Najeriya da kuma ƙarfafa haɗin kan al’umma.

Haka kuma, ya yabawa jagorancin Sarkin Zazzau, yana mai cewa sarakunan gargajiya na taka muhimmiyar rawa wajen tallafa wa gwamnati wajen samar da ci gaba mai ɗorewa da zaman lafiya tsakanin al’umma.
Da yake mayar da martani, Mai Martaba Sarkin Zazzau, Malam Ahmed Nuhu Bamalli, ya ce ziyarar ta sake tabbatar da ɗorewar alaƙar da ke tsakanin masarautun gargajiyar Najeriya tare da nuna ƙudurin su na haɗa kan ƙasa.

Ya bayyana cewa dangantakar tarihi tsakanin Masarautun Zazzau da Gombe ta samo asali tun daga ƙarni na 19, a lokacin juyin juya halin Musulunci na Shehu Usmanu Ɗanfodiyo, wanda ya bunƙasa shugabanci nagari, ilimi da zaman lafiya a Arewacin Najeriya.

Sarkin Zazzau ya kuma yi kira ga ‘yan Najeriya da su rungumi haɗin kai da haƙuri da juna, yana mai jaddada cewa sarakunan gargajiya za su ci gaba da jajircewa wajen inganta zaman lafiya, ilimi, ci gaban al’umma da haɗin kan ƙasa.

Afrika, Labarai, Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu, Najeriya, Nishadi, Sauran Duniya

Post navigation

Previous Post: Gombe Ta Yi Kira Ga Jami’o’i Su Tallafa Wa Gwamnati Ta Hanyar Bincike Da Ƙirƙire-ƙirƙire
Next Post: Matar El-Rufai Ta Roƙi Tinubu Ya Tabbatar An Yi Wa Mijinta Adalci

Karin Labarai Masu Alaka

APC Ta Ayana Tsohon Gwamnan Bauchi M.A Abubakar A Matsayin Dan Takarar Gwamna Afrika
Ankara Kai Wani Harin Bom Birnin Maiduguri Afrika
An Gudanar Da Zanga-Zanga A Guinea-Bissau Afrika
Ana Jimamin Mutuwar Giwa Mai Shekaru Kusan 60 A Kasar Kenya Sauran Duniya
Janar Christopher Zai Maye Gurbin Ministan Tsaron Najeriya Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Rasha: Zamu Ba Gwamnatin Venezuel Gudunmawa Sauran Duniya

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Sojojin Najeriya Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda Da Dama
  • An Sace Wani Shugaban Karamar Hukuma A Jihar Zamfara
  • Aikin Tsaftar Muhalli Na Wata-Wata Ya Samu Gagarumar Nasara A Gombe
  • Tinubu Ya Sake Fasalin Rundunar Sojin Ƙasa Domin Inganta Tsaro
  • Gombe Ta Haɗa Kai Da UNICEF Don Kare Yara Daga Tamowa Tun Kafin Haihuwa

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Zelensky: Gabas Ta Tsakiya Na Iya Nuna Makomarmu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Matsayar Iran Na Kera Makamin Nuclear Bazai Sanja Ba Afrika
  • Amurka Tana Cigaba Da Kare Jami’in Da Ya Kashe Ba Amurke Amurka
  • Ana Sa Ran FIFA Za Ta Yanke Hukunci Kan Karar Da Najeriya Ta Shigar Kan DR Congo Wasanni
  • Ma’aikatar Harkokin Wajen Amurka Ta Saka Takunkumi Visa Ga Wasu ‘Yan Rwanda Afrika
  • Kotu A Najeriya Ta Kame Mutane Bisa Zargin Ta’addaci Afrika
  • Zamfara: Sai Mun Hada Kai Don Kawo Karshen Ta’addanci Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnatin Gombe Ta Raba Naira Miliyan 14 Ga Iyalen ‘Yan Jaridan Da Suka Rasu Najeriya
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.