Gwamnonin jihohin Arewacin Najeriya sun ƙaddamar da Kwamitin Amintattu na Asusun Tsaron Arewacin Najeriya (Northern Nigeria Security Trust Fund), inda suka bayyana matakin a matsayin wani muhimmin yunƙuri na ƙarfafa yaƙi da matsalar tsaro ta hanyar haɗin gwiwa da samar da ingantaccen tallafi.
Shugaban Ƙungiyar Gwamnonin Jihohin Arewa kuma Gwamnan Jihar Gombe, Muhammadu Inuwa Yahaya, ne ya bayyana hakan yayin taron ƙungiyar da kuma ƙaddamar da kwamitin a ranar Laraba a Kaduna.
Ya ce an kafa Asusun Tsaron ne domin ya kasance mai taimaka wa ƙoƙarin Gwamnatin Tarayya wajen magance matsalolin tsaro da suka haɗa da ta’addanci, fashi da makami, garkuwa da mutane, shaye-shayen miyagun ƙwayoyi da sauran laifuffuka da ke barazana ga rayuka, dukiyoyi da ci gaban tattalin arzikin Arewacin Najeriya.
Gwamnan ya bayyana cewa asusun zai kasance wata hanya ta tattara kuɗaɗe, ƙarfafa musayar bayanan sirri, inganta haɗin gwiwar hukumomin tsaro da kuma tallafa wa ayyukan tsaro a tsakanin jihohin Arewa da hukumomin tsaro na tarayya.
Ya ƙara da cewa an zaɓi mambobin Kwamitin Amintattu ne daga jihohin Arewa bisa ƙwarewa da nagarta, kuma ana sa ran za su tabbatar da gaskiya, riƙon amana da ingantaccen gudanar da kuɗaɗen asusun tare da tsara ayyukan da za su inganta tsaro a yankin.

Muhammadu Inuwa Yahaya ya jaddada cewa bai kamata asusun ya zama wata sabuwar cibiyar gudanarwa da ke gudanar da taruka kawai ba, sai dai ya kasance wata kafa da za ta samar da sakamako mai ma’ana wajen kare rayuka da dukiyoyin al’umma.
Ya tunatar da cewa tun a baya Gwamnonin Arewa sun amince kowace jiha tare da ƙananan hukumominta za su rika bayar da naira biliyan ɗaya duk wata na tsawon watanni 12 domin tallafa wa asusun. Ya yabawa jihohin da suka fara cika alƙawarinsu tare da kira ga sauran jihohi su gaggauta biyan gudummawar da suka ɗauka.
Gwamnan ya kuma sake bayyana goyon bayan Gwamnonin Arewa ga Shugaban Ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, da ƙoƙarin Gwamnatin Tarayya wajen dawo da zaman lafiya a ƙasar, tare da nuna goyon baya ga tattaunawar da ake yi kan kafa ‘yan sandan jihohi domin ƙarfafa tsarin tsaro.
Haka kuma ya jaddada buƙatar magance tushen matsalolin tsaro ta hanyar zuba jari a fannonin ilimi, noma, samar da ayyukan yi, ƙarfafa matasa da koyar da sana’o’i, yana mai cewa matakan tsaro kaɗai ba za su wadatar wajen kawo ƙarshen matsalar ba.
Ya yi kira ga sarakunan gargajiya, shugabannin addinai, shugabannin al’umma, ƙungiyoyin fararen hula, masu zaman kansu da abokan hulɗar ci gaba da su mara wa wannan shiri baya, yana mai cewa tabbatar da tsaro nauyi ne da ya rataya a wuyan kowa.

Gwamna Muhammadu Inuwa Yahaya ya bayyana kwarin gwiwar cewa idan aka haɗa kai tare da nuna jajircewa da cika alƙawura, Asusun Tsaron Arewacin Najeriya zai taimaka wajen inganta haɗin gwiwar tsaro da samar da zaman lafiya, kwanciyar hankali da ci gaba mai ɗorewa a yankin Arewa.


