Gwamnan jihar Jigawa a Najeriya Malam Umar Namadi, ya amince da naɗin, Dakta Lawan Ahmed Muhammad Sani, a matsayin Sarkin Gumel na 17.
Sakataren Gwamnatin jihar Jigawa, Malam Bala Ibrahim, ne ya sanar da naɗin ta cikin wata sanarwa da ya sanya wa hannu, inda ya ce naɗin ya biyo bayan shawarar da Majalisar Masu Zaɓen Sarkin Gumel da Majalisar Sarakunan jihar Jigawa suka gabatar wa gwamnan.
Kafin naɗinsa ya kasance shi ne Chiroman Gumel, sannan yana riƙe da muƙamin Daraktan Tsaron Intanet na Hukumar Bunƙasa Fasahar Sadarwa ta Najeriya (NITDA).
Dakta Lawan dai ya gaji mahaifinsa, Alhaji Ahmed Muhammad Sani II, ne wanda ya rasu a ranar Alhamis, 3 ga Satumban shekarar 2026, bayan shafe shekaru 46 yana mulkin Masarautar Gumel.


