NFF Ta Nemi Afuwar Tinubu da ’Yan Najeriya Kan Rashin Samun Tikitin Kai Tsaye Zuwa Gasar Kofin Duniya ta Mata
Hukumar Kwallon Ƙafa ta Najeriya (NFF) ta bayyana matuƙar nadama tare da neman afuwar Shugaba Bola Ahmed Tinubu da al’ummar Najeriya bayan da Super Falcons ta kasa samun tikitin kai tsaye zuwa gasar cin kofin duniya ta FIFA ta mata ta shekarar 2027.
Shugaban NFF, Alhaji Ibrahim Musa Gusau, ne ya bayyana hakan a madadin kwamitin zartarwa na hukumar, ’yan wasan Super Falcons da kuma daukacin iyalan ƙwallon ƙafar Najeriya.
NFF ta ce tana sane da irin takaicin da sakamakon ya jefa miliyoyin ’yan Najeriya da ke matuƙar goyon bayan Super Falcons, tana mai cewa ƙungiyar ta shiga gasar ne ɗauke da burin al’umma da kuma gagarumin goyon bayan gwamnatin tarayya.
Hukumar ta kuma miƙa takamaiman uzurinta ga Shugaba Tinubu bisa abin da ta bayyana a matsayin wannan abin takaici.
NFF ta ce Shugaba Tinubu ya nuna gagarumin ƙuduri wajen tallafawa harkokin wasanni a Najeriya, musamman bunƙasa da jin daɗin mata masu harkar wasanni.
Ta tuna da irin karramawa da kyaututtukan da gwamnatin Tinubu ta bai wa Super Falcons bayan nasarar da ta samu a gasar WAFCON da ta gabata, waɗanda suka haɗa da kyaututtukan kuɗi, lambobin yabo na ƙasa, gidaje da kuma liyafar musamman da aka shirya domin ƙungiyar.
A cewar NFF, waɗannan abubuwa ba wai kawai kyaututtuka ne na abin duniya ba, illa sun nuna irin darajar da Shugaban Ƙasa ke bai wa ’yan wasa da kuma yadda yake ganin wasanni a matsayin wata hanya ta haɗa kan ’yan Najeriya da kuma ƙarfafa musu gwiwa.
- Hukumar ta ce saboda haka tana me amincewa cikin tawali’u da nadama da sakamakon da bashi ake tsammani ba a wannan mataki na gasar.
NFF ta kuma nemi afuwar Majalisar Ƙasa, Hukumar Kula da Wasanni ta Ƙasa, masu ɗaukar nauyin ƙungiyar, masu ruwa da tsaki da kuma miliyoyin magoya bayan Super Falcons a Najeriya da sauran sassan duniya.
Sai dai hukumar ta jaddada cewa har yanzu akwai wata damar samun gurbin shiga gasar ta 2027 ta hanyar wasannin neman gurbin CAF.
Ta ce Super Falcons za ta fafata domin samun ɗaya daga cikin tikiti biyu da ake da su a matakin **CAF play-off**, sannan ta nemi cancantar shiga gasar cin kofin duniya ta hanyar **FIFA play-off tournament**.
NFF ta ce yanzu abin da ya fi muhimmanci shi ne ƙungiyar ta sake haɗa ƙarfi, ta koyi darussa daga wannan koma baya sannan ta mayar da hankali gaba ɗaya kan damar da ta rage.
Hukumar ta ƙara da cewa za ta gudanar da cikakken bincike kan shirye-shiryen ƙungiyar, tsare-tsaren fasaha, harkokin sufuri da sauran ayyukan da suka shafi gasar, domin gano wuraren da ke buƙatar gyara da ingantawa.
NFF ta ce ta ji takaicin ’yan Najeriya kuma tana tare da su a cikin wannan yanayi, tare da amincewa da alhakin da ke kanta.
Hukumar ta ce ba za ta karaya ba, tana mai ƙudurin ganin Super Falcons ta dawo da ƙarfi, ta ƙara jajircewa tare da yin duk mai yiwuwa domin faranta wa Shugaban Ƙasa, gwamnatin tarayya da al’ummar Najeriya rai.
NFF ta kuma gode wa ’yan Najeriya bisa ci gaba da nuna goyon baya ga Super Falcons, tare da kira gare su da su ci gaba da kasancewa tare da ƙungiyar yayin da take ƙoƙarin amfani da sauran hanyar da ta rage domin samun gurbin shiga **Gasar Kofin Duniya ta FIFA ta Mata ta 2027**.


