Tsohon Gwamnan jihar Gombe kuma Sanata mai wakiltar Gombe ta Tsakiya, Muhammad Danjuma Goje, ya ce har yanzu yana cikin jam’iyyar APC, yana kuma tuntubar masu ruwa da tsaki kan makomar siyasarsa.
Goje ya bayyana hakan ne a ranar Asabar a gidansa da ke Pantami, Gombe, lokacin da magoya bayansa da abokan siyasa suka kai masa ziyara.
Wannan na zuwa ne a daidai lokacin da ake ci gaba da samun rade-radin cewa tsohon gwamnan na fuskantar matsin lamba daga magoya bayansa da ke son ya sake neman kujerar Sanata a zaben 2027, bayan da bai samu tikitin APC a zaɓen fidda gwani na Sanatan Gombe ta Tsakiya ba.
Duk da rahotannin da ke cewa jam’iyyar PDP na matsa masa ya koma cikinta, Goje ya bayyana karara cewa bai sauya sheka zuwa wata jam’iyya ba.
Ya ce, “Ban sauya sheka zuwa wata jam’iyya ba. Har yanzu ina cikin APC,” sannan ya bukaci magoya bayansa su ci gaba da haɗin kai, tare da bai wa masu ruwa da tsaki na siyasa hadin kai da biyayya.
Sai dai tsohon gwamnan ya bar kofar sake neman kujerar Sanata a bude, inda ya bayyana cewa tun farko bai shirya sake tsayawa takara ba, amma matsin lambar magoya bayansa na sa shi sake tunani.
Goje ya ce ya shafe shekaru 45 yana harkokin siyasa, inda ya rike mukamai daban-daban a matakin jiha da kasa, ciki har da shugabancin Kwamitin Kasafin Kudi na Majalisar Dattawa.
Ya jagoranci jihar Gombe a matsayin gwamna na tsawon wa’adi biyu daga shekarar 2003 zuwa 2011, sannan ya zama Sanatan Gombe ta Tsakiya tun shekarar 2011.
An sake zabar Goje a matsayin Sanata a shekarun 2015, 2019 da 2023, abin da ke nufin idan ya sake tsayawa takara a 2027, zai kasance neman wa’adi na biyar a Majalisar Dattawa.
A zaben fidda gwani na APC da aka gudanar a watan Mayun 2026, Mohammed Ahmed, tsohon Mataimakin Kwamishinan ’Yan Sanda, ya samu tikitin jam’iyyar na Gombe ta Tsakiya.
Sai dai Goje ya yi watsi da sakamakon zaben fidda gwanin, inda ya bayyana shi a matsayin na bogi tare da cewa za a fitar da sahihin sakamako a Abuja. Daga bisani, ba a samu sunansa cikin jerin ‘yan takarar Majalisar Dokoki ta Kasa da APC ta mika wa Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Kasa, INEC ba.
Wannan ci gaba ya kara haifar da rade-radin cewa Goje na iya neman kujerar Gombe ta Tsakiya a karkashin wata jam’iyya.
Rahotanni sun kuma nuna cewa PDP da African Democratic Congress, ADC, na zawarcin tsohon gwamnan, yayin da ake alakanta yiwuwar komawarsa PDP da batun neman kujerar Sanata da kuma goyon bayan dan takarar gwamnan jihar na PDP, Farfesa Isa Ali Ibrahim Pantami.
Sai dai PDP ta riga ta tsayar da Aliyu Hammadu a matsayin dan takararta na Sanatan Gombe ta Tsakiya, lamarin da zai iya haifar da sauye-sauye a cikin tsarin jam’iyyar idan Goje ya yanke shawarar neman tikitin.
A nasa bangaren, Goje ya jaddada muhimmancin biyayya da hadin kai tsakanin magoya bayansa, yana mai cewa ya kamata ‘yan siyasa su hada kai domin cimma manufofin da suka dace.
Ya kuma bayyana cewa tasirinsa a siyasar jihar ya wuce jam’iyyar APC, inda ya ce ya horar da ‘yan siyasa daga manyan jam’iyyun siyasa daban-daban a Gombe a tsawon shekarun da ya shafe yana siyasa.
Ya ce, “Mutane daga dukkanin manyan jam’iyyun siyasa a jihar Gombe sun kasance wadanda na yi wa jagoranci a siyasa.”


