Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Maryam Dan’azumi Ta Koma Gida Bayan Zama Gwarzuwar Gasar Alƙur’ani Afrika
  • Goje Yace Bai Sauya Sheka Ba, Yana Shawara Kan Makomar Siyasar 2027 Afrika
  • Najeriya: Gombe ‘Yan Sanda Sun Kammala Bikin Ranar Matasa Da Dasa Itatuwa Domin Makoma Mai Ɗorewa Afrika
  • Inuwa Yahaya Zai Jagoranci Tattara Masu Ruwa da Tsaki Na APC A Arewa Maso Gabashin Najeriya Afrika
  • APC Ta Tsayar Da Usman Maijama’a Kallamu A Zaɓen Cike Gurbi Na Gombe, Kwami Da Funakaye Afrika

Miliyan Biyar Ko Rayuwata: Barazanar ’Yan Ta’adda Ta Jefa Wani Mazaunin Dukku Cikin Fargaba
Published: August 18, 2026 at 4:13 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Alhaji Musa Gurya wanda mazaunin kauyen Malala ne da ke karamar hukumar Dukku a jihar Gombe ya bayyana cewa rayuwarsa ta na cikin hatsari bayan wasu ‘yan ta’adda sun kai farmaki gidansu su ka kashe kaninsa amma shi Allah ya kubutar da shi bayan sun bi shi don kashe shi amma ba su samu nasara.

Musa Gurya ya ce a lokacin ‘yan ta’addan sun dauke wayoyin salularsu 4 da babur dinsa sabo da ya saya “a daren karfe 1:30am na kira DPO na Dukku na shaida ma sa abun da ya faru kuma shi da kansa ya zo a ka dauki gawar kanina tare da shi zuwa Malala inda mu ka yi ma sa jana’iza.”

Alhaji Musa ya cigaba da cewa bayan wata daya da aukuwar akasin sai barayin su ka sake kiran sa su na ma sa barazana ko ya ba su kudi Naira miliyan 5 ko su kashe shi.

Hakanan dai ya yi ta musayar magana da su. Gurya ya ce ya kai rahoto wajen DPO na Dukku inda a ka bi wayar da barayin ke aiki da ita inda a ka samu kama daya daga cikinsu mai suna Dauda. DPO ya tura batun zuwa CID “na kasha kimanin Naira miliyan 5 kan batun amma rana tsaka na ji an sake Dauda ba tare da zuwa kotu ba”

Alhaji Musa Gurya ya yi zargin da cewa da alamu su Dauda sun ba da wani kasafi ne a ka kyale su. Kazalika Gurya ya ce kwamshinan ‘yan sanda na Gombe ya na da masaniya kan akasin.

“Gaskiya ni da sauran ‘yan uwana mu na cikin tashin hankali ba ma iya barci da ido biyu.”

A Kokarin da mukayi Saboda Jin tabakin Jami’in Hulda da jama’a na rundunar ‘yan Sandar jihar Gombe DSP Buhari Abdullahi yaci Tura, inda ya bayyana cewa Suna Gudanar da bincike Akan lamarin.

Afrika, Labarai, Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu, Najeriya, Sauran Duniya, Tsaro

Post navigation

Previous Post: KADCCAM Ta Yaba Da Shuka Bishiyoyi A Kaduna
Next Post: An Yi Barazanar Kaurace Wa Gasar Cin Kofin Duniya

Karin Labarai Masu Alaka

Haɗin Gwiwar GOSERC Da Savannah Zai Ƙarfafa Rarraba Wutar Lantarki A Faɗin Jihar Gombe Afrika
Isra’ila Takai Sabon Hari Tehran Ranar Lahadi Labarai
Gwamnan Gombe Ya Ƙara Tallafin N148.76bn Domin Aiwatar da Sabon Tsarin Albashi A Jami’ar Gombe Afrika
Taron Masu Mu’amala Da Kafar Facebook A Kano Afrika
Dangote Ya Rage Farashin Mai A Najeriya Labarai
Tinubu Ya Buɗe Katafaren Kamfanin Sarrafa Lithium Domin Bunƙasa Tattalin Arziki Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Magoya Bayan Liverpool Sun Bukaci Iraola Ya Ɗauki Mataki Mai Tsauri Kan Szoboszlai
  • Tottenham Tana Da Damar Ɗaukar Ɗan Wasan Gefe Na Chelsea, Mykhailo Mudryk.
  • Maryam Dan’azumi Ta Koma Gida Bayan Zama Gwarzuwar Gasar Alƙur’ani
  • Goje Yace Bai Sauya Sheka Ba, Yana Shawara Kan Makomar Siyasar 2027
  • Nigeria Ta Samu Tikitin Gasar Wasan Beach Volleyball A Olympics Los Angeles 2028

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Hawan Babbar Sallah A Masarautar Kaltungo Dake Jihar Gombe Afrika
  • Dakarun Zaman Lafiya Na Majalisar Dinkin Duniya Sun Rasa Rayukan Su Afrika
  • Za’a Fuskanci Bala’in Yunwa A Najeriya Labarai
  • Kwamitin Ardo Chindo Ya Buƙaci A Hana Mamaye Filayen Kiwo da Gandun Daji Afrika
  • Gobara Mafi Muni Cikin Shekaru 60 A Hong Kong Ta Hallaka Rayuka Sauran Duniya
  • Hukumar Tsaron Civil Defence A Gombe Ta Samar Da Jami’ai Don Tabbatar Da Tsaro A Bukukuwan Karshen Shekara Labarai
  • Magajin Garin Istanbul Dake Kurkuku Ya Bukaci A Gudanar Da Zabe Labarai
  • Anfara Tantance Lafiyar Maniyyatan Jihar Gombe Kiwon Lafiya
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.