Alhaji Musa Gurya wanda mazaunin kauyen Malala ne da ke karamar hukumar Dukku a jihar Gombe ya bayyana cewa rayuwarsa ta na cikin hatsari bayan wasu ‘yan ta’adda sun kai farmaki gidansu su ka kashe kaninsa amma shi Allah ya kubutar da shi bayan sun bi shi don kashe shi amma ba su samu nasara.
Musa Gurya ya ce a lokacin ‘yan ta’addan sun dauke wayoyin salularsu 4 da babur dinsa sabo da ya saya “a daren karfe 1:30am na kira DPO na Dukku na shaida ma sa abun da ya faru kuma shi da kansa ya zo a ka dauki gawar kanina tare da shi zuwa Malala inda mu ka yi ma sa jana’iza.”
Alhaji Musa ya cigaba da cewa bayan wata daya da aukuwar akasin sai barayin su ka sake kiran sa su na ma sa barazana ko ya ba su kudi Naira miliyan 5 ko su kashe shi.
Hakanan dai ya yi ta musayar magana da su. Gurya ya ce ya kai rahoto wajen DPO na Dukku inda a ka bi wayar da barayin ke aiki da ita inda a ka samu kama daya daga cikinsu mai suna Dauda. DPO ya tura batun zuwa CID “na kasha kimanin Naira miliyan 5 kan batun amma rana tsaka na ji an sake Dauda ba tare da zuwa kotu ba”
Alhaji Musa Gurya ya yi zargin da cewa da alamu su Dauda sun ba da wani kasafi ne a ka kyale su. Kazalika Gurya ya ce kwamshinan ‘yan sanda na Gombe ya na da masaniya kan akasin.
“Gaskiya ni da sauran ‘yan uwana mu na cikin tashin hankali ba ma iya barci da ido biyu.”
A Kokarin da mukayi Saboda Jin tabakin Jami’in Hulda da jama’a na rundunar ‘yan Sandar jihar Gombe DSP Buhari Abdullahi yaci Tura, inda ya bayyana cewa Suna Gudanar da bincike Akan lamarin.


