Gwamnonin Arewa, karkashin jagorancin Shugaban Northern Nigeria Governors’ Forum (NNGF) kuma Gwamnan jihar Gombe, Muhammadu Inuwa Yahaya, sun mika sakon ta’aziyya ga al’ummar Jihohin Jigawa da Zamfara bisa rasuwar Sarakunan Gumel da Zurmi.
Gwamna Inuwa Yahaya ya bayyana rasuwar Mai Martaba Sarkin Gumel, Alhaji Ahmad Muhammad Sani II, a matsayin babban rashi ga Jihar Jigawa, Arewa da Najeriya baki daya.
Ya ce marigayin ya kasance basarake mai mutunci, wanda zamaninsa ya kasance cike da hikima, tawali’u, kokarin samar da zaman lafiya da kuma jajircewa wajen inganta rayuwar al’ummarsa.
Gwamnan ya bayyana cewa Sarkin Gumel ya bayar da muhimmiyar gudunmawa wajen tabbatar da zaman lafiya, hadin kai da ci gaban Masarautar Gumel, inda ya bar tarihi da za a ci gaba da tunawa da shi.
A cikin sakon ta’aziyyar da ya fitar a madadin gwamnonin Arewa, Inuwa Yahaya ya jajanta wa iyalan marigayin, Majalisar Masarautar Gumel, al’ummar masarautar da kuma Gwamnati da al’ummar Jihar Jigawa.
Ya bukaci iyalan marigayin da al’ummar masarautar su samu kwanciyar hankali ta hanyar tunawa da kyawawan halaye da gadon da ya bari, musamman zaman lafiya, hadin kai, hidima ga al’umma da ci gaba.
Haka kuma, Shugaban NNGF din ya bayyana alhini kan rasuwar Mai Martaba Sarkin Zurmi na Jihar Zamfara, Alhaji Bello Sulaiman.
Inuwa Yahaya ya bayyana marigayin a matsayin basarake mai mutunci kuma mai kishin al’ummarsa, wanda ya sadaukar da shekaru biyar da ya yi kan karagar mulki wajen tabbatar da zaman lafiya, hadin kai da jin dadin jama’ar masarautar.
Ya ce rasuwar Sarkin Zurmi babban rashi ne ga Masarautar Zurmi, Jihar Zamfara da kuma daukacin tsarin sarautun gargajiya na Arewacin Najeriya.
Gwamnan ya mika sakon ta’aziyyarsa ga iyalan marigayin, Majalisar Masarautar Zurmi, al’ummar masarautar da Gwamnati da al’ummar Jihar Zamfara, yana mai kira da su samu karfin guiwa daga kyawawan ayyuka da tarihin da marigayin ya bari.
Ya yi addu’ar Allah Ya gafarta wa sarakunan biyu kura-kuransu, Ya karbi kyawawan ayyukansu, Ya sanya su cikin rahamarSa, Ya kuma ba su Aljannatul Firdaus.
Rasuwar Sarkin Zurmi ta faru ne a ranar Litinin, bayan shekaru biyar da hawansa karagar mulki.


