Kungiyar Kare Hakkin ’Yan Jarida ta Duniya (RSF) ta bukaci hukumomin Nijar da su gaggauta gudanar da bincike domin gano inda fitaccen dan jarida Moussa Kaka yake, bayan da aka rasa jin duriyarsa tun ranar 31 ga Agusta, 2026.
A cewar RSF, Kaka, wanda shi ne Darakta-Janar na gidan rediyo da talabijin na Radio Télévision Saraounia (RTS), ya bar ofishinsa da ke birnin Yamai da misalin ƙarfe 7 na yamma a ranar 31 ga Agusta domin komawa gida, amma bai isa ba. Tun daga lokacin iyalansa da abokan aikinsa ba su iya samun tuntubarsa ba.
RSF ta bayyana damuwa kan bacewar ɗan jaridar, musamman ganin yadda ake fuskantar yanayin siyasa da tsaro mai ɗan zafi a Nijar. Kungiyar ta bukaci hukumomin ƙasar da su gaggauta gano shi tare da tabbatar da tsaronsa da kuma binciken yanayin da ya jawo bacewarsa.
Moussa Kaka ya dade yana aikin jarida a Nijar, kuma a baya ya taba kasancewa wakilin Radio France Internationale (RFI) a ƙasar.


