Hukumar Zaɓe Mai Zaman Kanta ta a Najeriya wato INEC, ta ce ta kammala shirye-shiryenta domin gudanar da zaɓen cike gurbin kujerar Majalisar Wakilai ta Tarayya mai wakiltar Gombe, Kwami da Funakaye, wanda za a gudanar ranar Asabar.
Kwamishinan Zaɓe na jihar Gombe, Alhaji Umar Mukhtar Gajiram, ne ya bayyana hakan yayin taron Kwamitin Tuntuɓa kan Tsaron Zaɓe na Ƙungiyoyin Hukumomin Tsaro, ICCES, da aka gudanar domin duba shirye-shiryen zaɓen.
Alhaji Gajiram ya ce hukumar ta karɓi dukkan kayan zaɓe marasa muhimmanci da ake buƙata, yayin da aka kammala horas da jami’an kula da masu jagorantar rumfunan zaɓe, wato Supervisory Presiding Officers.
Ya ƙara da cewa ana ci gaba da horas da Presiding Officers da Assistant Presiding Officers, yayin da hukumar ke jiran isowar kayan zaɓe masu muhimmanci.
Kwamishinan ya jaddada buƙatar samar da isasshen tsaro domin kare jami’an INEC da kayan zaɓe a rumfunan zaɓe 903 da ke faɗin ƙananan hukumomin Gombe, Kwami da Funakaye.
Ya bayyana Gombe da Funakaye a matsayin wuraren da ake ɗauka a matsayin masu haɗarin tsaro, sakamakon ayyukan ’yan daba masu alaƙa da siyasa.
Saboda haka, ya yi kira ga hukumomin tsaro da su ƙara kaimi wajen tattara bayanan sirri, gano alamun barazana tun da wuri da kuma gaggauta ɗaukar matakin da ya dace idan wata barazana ta taso.
Shi ma da yake magana, Kwamishinan ’Yan Sandan Jihar Gombe, kuma mataimakin shugaban kwamitin ICCES, CP Umar Ahmed Chuso, ya ce an ɗauki matakan tsaro na riga-kafi domin magance matsalolin tsaro da aka gano kafin da kuma lokacin zaɓen.
CP Chuso ya yi kira ga jam’iyyun siyasa da magoya bayansu da su gudanar da harkokinsu cikin lumana, yana mai gargadin cewa jami’an tsaro ba za su lamunci duk wani abu da zai iya kawo cikas ga gudanar da zaɓen cikin kwanciyar hankali ba.
Taron INEC da ICCES ya haɗa wakilan hukumomin tsaro da sauran hukumomin da abin ya shafa, domin ƙarfafa haɗin gwiwa da tabbatar da gudanar da zaɓen cike gurbin cikin lumana, gaskiya da sahihanci ranar Asabar.


