Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Gwamnatin Sokoto Ta Kafa Kwamitin Malamai Don Binciken Rikicin Addini Afrika
  • Inuwa Ya Bukaci A Kara Zuba Jari A Ilimin Sana’o’i Domin Samar Wa Matasa Aikin Yi Afrika
  • Gwamnonin Arewa Sun Yi Jimamin Rasuwar Bamanga Tukur, Sun Yaba Da Gudunmawarsa Ga Najeriya Afrika
  • Tsohon Shugaban PDP, Bamanga Tukur, Ya Rasu Yana da Shekaru 91 Afrika
  • Filato: Gwamnati Ta Ƙarfafa Matakan Kariya Yayin Sake Buɗe Makarantu Afrika

Kebbi Ta Ce Sama Sa Maniyyata 3,000 Ne Suka Biya Naira Biliyan 21.5 Na Kujerun Hajji
Published: September 15, 2026 at 9:29 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Gwamnatin jihar Kebbi a arewacin Najeriya ta ƙaryata rahoton da ya ce ta sayi kujerun Hajji har na Naira biliyan 21.5 domin taɓawa ga ƴan jihar.

Hajj Reporters ta rawaito cewa wani mai suna Evangelist Ibrahim Dikko ne ya yi zargin cewa gwamnatin jihar ta kashe waɗannan maƙudan kuɗaɗe don rabawa mutane kujerun aikin Hajji.

A wata sanarwa da Babban Sakataren Yaɗa Labarai na Gwamnan jihar, Ahmed Idris ta fitar, gwamnatin ta ce sam wannan rahoto ƙarya ne domin kuɗin da ake magana akai, na kujeru ne da maniyyata su ka biya.

“An ja hankalinmu kan wani labari da Evangelist Ibrahim Dikko ya wallafa, inda ya yi zargin cewa Gwamnatin Jihar Kebbi ta ware sama da Naira biliyan 21.5 domin daukar nauyin alhazan jihar zuwa Ƙasa Mai Tsarki.

“Muna son bayyana wa a fili cewa wannan zargi ba gaskiya ba ne, kuma ya ƙunshi bayanan da za su iya yaudarar jama’a da kuma rashin sahihanci.

” Domin magance duk wata shakka, Gwamnatin Jihar Kebbi ba ta ware Naira biliyan 21.5, ko wani adadin kuɗi, domin ɗaukar nauyin aikin Hajjin 2027 ba.

” Kuɗaɗen da aka ambata a cikin labarin, kuɗaɗe ne da kowane maniyyaci zuwa aikin ya biya domin biyan kujerar Hajji.

“Naira biliyan 21.5 da Hukumar Jin Daɗin Alhazai ta Jihar Kebbi ta tura, na wakiltar kuɗaɗen da sama da maniyyata 3,000 da ke shirin zuwa aikin Hajjin 2027 suka biya,” in ji Idris.

Ya kara da cewa hukumar na aiki ne a matsayin hanyar da ake bi wajen karɓa, sarrafawa da kuma tura kuɗaɗen da maniyyata su ka biya zuwa Hukumar Alhazai ta Ƙasa ta Najeriya (NAHCON).

Ya ƙara da cewa ba a yi amfani da kuɗaɗen gwamnati ko wani kaso daga cikin kasafin kuɗin jihar wajen biyan waɗannan kuɗaɗen Hajji na kowane mutum ba.

Afrika, Labarai, Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu, Najeriya, Sauran Duniya

Post navigation

Previous Post: Inuwa Ya Bukaci A Kara Zuba Jari A Ilimin Sana’o’i Domin Samar Wa Matasa Aikin Yi
Next Post: Gwamnatin Sokoto Ta Kafa Kwamitin Malamai Don Binciken Rikicin Addini

Karin Labarai Masu Alaka

Likitoci Masu Neman Kwarewa Zasu Shiga Yakin Aiki Afrika
Gwamnatin Tarayya Za Ta Sake Fasalin Shirin NYSC Afrika
Gwamnatin Najeriya Ta Dauki Matakai Don Farfaɗo Da Maɗaba’ar Gwamnati Labarai
Gwamnatin Najeriya Ta Karyata Raɗe-Raɗin Canza Sunan Kasar Da Soke Shari’a A Arewa Afrika
An Sace Wani Shugaban Karamar Hukuma A Jihar Zamfara Afrika
Dusar Kankara Ta Hana Jirage Tashi A Birnin Paris Labarai

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Gwamnatin Sokoto Ta Kafa Kwamitin Malamai Don Binciken Rikicin Addini
  • Kebbi Ta Ce Sama Sa Maniyyata 3,000 Ne Suka Biya Naira Biliyan 21.5 Na Kujerun Hajji
  • Inuwa Ya Bukaci A Kara Zuba Jari A Ilimin Sana’o’i Domin Samar Wa Matasa Aikin Yi
  • Gwamnonin Arewa Sun Yi Jimamin Rasuwar Bamanga Tukur, Sun Yaba Da Gudunmawarsa Ga Najeriya
  • Tsohon Shugaban PDP, Bamanga Tukur, Ya Rasu Yana da Shekaru 91

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Wasu Zakaru Da Suka Samu Karramawar Hukumar CAF Ta Afrika Wasanni
  • Gwamnatin Filato Ta Gurfanar Da Maharan Rukuba A Kotu Afrika
  • Tinubu: Munsayi Jiragen Yaki Daga Wajen Amurka Amurka
  • Amurkawa Sun Nuna Bacin Rai Saboda Yawaita Kashe ‘Yan Kasar Amurka
  • Bisa Alamu Hadinkan Kasashen Yankin Sahel Zai Haifar Da Nagarta Afrika
  • Shugabannin Kasar Australia Sun Bukaci ‘Yan Kasar Suyi Zanga Zanga Cikin Lumana Afrika
  • Jami’an tsaro sama da dubu biyar ne zasuyi aikin tabbatar da tsaro Alokacin bikin karamar sallah a Jihar Nejan Najeriya. Najeriya
  • Gwamnan Jihar Gombe Ya Ƙarfafa Wa Sabbin Masu Ashaka Cement Gwiwar Samar Da Ayyukan Yi Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.