Gwamnatin jihar Kebbi a arewacin Najeriya ta ƙaryata rahoton da ya ce ta sayi kujerun Hajji har na Naira biliyan 21.5 domin taɓawa ga ƴan jihar.
Hajj Reporters ta rawaito cewa wani mai suna Evangelist Ibrahim Dikko ne ya yi zargin cewa gwamnatin jihar ta kashe waɗannan maƙudan kuɗaɗe don rabawa mutane kujerun aikin Hajji.
A wata sanarwa da Babban Sakataren Yaɗa Labarai na Gwamnan jihar, Ahmed Idris ta fitar, gwamnatin ta ce sam wannan rahoto ƙarya ne domin kuɗin da ake magana akai, na kujeru ne da maniyyata su ka biya.
“An ja hankalinmu kan wani labari da Evangelist Ibrahim Dikko ya wallafa, inda ya yi zargin cewa Gwamnatin Jihar Kebbi ta ware sama da Naira biliyan 21.5 domin daukar nauyin alhazan jihar zuwa Ƙasa Mai Tsarki.
“Muna son bayyana wa a fili cewa wannan zargi ba gaskiya ba ne, kuma ya ƙunshi bayanan da za su iya yaudarar jama’a da kuma rashin sahihanci.
” Domin magance duk wata shakka, Gwamnatin Jihar Kebbi ba ta ware Naira biliyan 21.5, ko wani adadin kuɗi, domin ɗaukar nauyin aikin Hajjin 2027 ba.
” Kuɗaɗen da aka ambata a cikin labarin, kuɗaɗe ne da kowane maniyyaci zuwa aikin ya biya domin biyan kujerar Hajji.
“Naira biliyan 21.5 da Hukumar Jin Daɗin Alhazai ta Jihar Kebbi ta tura, na wakiltar kuɗaɗen da sama da maniyyata 3,000 da ke shirin zuwa aikin Hajjin 2027 suka biya,” in ji Idris.
Ya kara da cewa hukumar na aiki ne a matsayin hanyar da ake bi wajen karɓa, sarrafawa da kuma tura kuɗaɗen da maniyyata su ka biya zuwa Hukumar Alhazai ta Ƙasa ta Najeriya (NAHCON).
Ya ƙara da cewa ba a yi amfani da kuɗaɗen gwamnati ko wani kaso daga cikin kasafin kuɗin jihar wajen biyan waɗannan kuɗaɗen Hajji na kowane mutum ba.


