Gwamnatin jihar Sokoto ta nesanta kanta daga duk wani mutum ko ƙungiya da ke fakewa da addini wajen batanci ko cin mutuncin Annabi Muhammad (SAW), iyayensa, iyalansa da sahabbansa.
Gwamnatin ta bayyana cewa tana ci gaba da jaddada cikakken biyayyarta, girmamawarta da mutuntawa ga fiyayyen halitta, Annabi Muhammad (SAW), da kuma iyalansa da sahabbansa.
A cikin wata sanarwa da Darakta-Janar na Yaɗa Labarai da Hulɗa da Jama’a na Gwamnatin jihar Sokoto, Abubakar Bawa, ya sanya wa hannu a fadar gwamnatin jihar a ranar 15 ga Satumba, 2026, gwamnatin ta yi kira ga al’ummar jihar da su ci gaba da nuna ƙauna, girmamawa da mutuntawa ga Annabi Muhammad (SAW).
Sanarwar ta zo ne bayan tashin-tashinar da ta faru a wasu sassan babban birnin Jihar Sokoto, wadda ake alakanta ta da batun addini.
Dangane da lamarin, gwamnatin jihar ta kafa wani kwamiti na malamai domin gudanar da bincike kan musabbabin rikicin, tare da bai wa gwamnatin shawarwari kan matakan da suka dace a ɗauka domin kare martaba da maslahar jihar.
Haka kuma, gwamnatin ta bayar da umarnin gudanar da cikakken bincike kan harin da aka kai da kuma kisan da ya faru a Masallacin Juma’a na Musa Lukuwa da ke Mabera.
Gwamnatin ta kuma bayar da umarnin rufe masallacin har zuwa wani lokaci, kasancewarsa wurin da aka aikata laifin, domin ba da damar gudanar da bincike kan lamarin.
A wani ɓangare na sanarwar, gwamnatin ta yi kira ga al’ummar jihar da su guji furta kalamai masu tayar da hankali ko waɗanda za su iya rura wutar rikici da tunzura jama’a.
Ta ce irin waɗannan kalamai na iya kawo cikas ga zaman lafiya da haɗin kan al’umma, waɗanda ta ce jihar Sokoto ta shahara da su.
Gwamnatin ta kuma tabbatar wa al’ummar jihar da cikakken kudirinta na kare rayuka da dukiyoyin jama’a da kuma tabbatar da zaman lafiya da tsaro a faɗin jihar.
Ta buƙaci jama’a da su ba jami’an tsaro da hukumomin da ke gudanar da bincike cikakken haɗin kai, tare da kauce wa duk wani mataki da zai iya ƙara dagula al’amura.


