Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Gwamnan Gombe Ya Taya Sarkin Musulmi Murnar Cika Shekaru 70, Ya Yi Masa Addu’ar Ƙarin Lafiya Da Tsawon Rai Afrika
  • Maryam Dan’azumi Ta Koma Gida Bayan Zama Gwarzuwar Gasar Alƙur’ani Afrika
  • Goje Yace Bai Sauya Sheka Ba, Yana Shawara Kan Makomar Siyasar 2027 Afrika
  • Najeriya: Gombe ‘Yan Sanda Sun Kammala Bikin Ranar Matasa Da Dasa Itatuwa Domin Makoma Mai Ɗorewa Afrika
  • Inuwa Yahaya Zai Jagoranci Tattara Masu Ruwa da Tsaki Na APC A Arewa Maso Gabashin Najeriya Afrika

An Gargaɗi Mazauna Maiduguri Su Guji Yaɗa Labaran Ƙarya
Published: March 13, 2026 at 5:12 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

An Gargaɗi Mazauna Maiduguri Su Guji Yaɗa Labaran Ƙarya

Daga Adamu Aliyu Ngulde, Maiduguri

An gargaɗi mazauna birnin Maiduguri da su guji wallafawa da kuma yaɗa labaran ƙarya a kafofin sadarwar zamani domin kauce wa haifar da tashin hankali a cikin al’umma.

Jami’in hulɗa da jama’a na rundunar ’yan sandan Jihar Borno, ASP Nahum Kenneth Daso, ya musanta rahotannin da ke yawo a kafofin sadarwar zamani da ke cewa an samu wani abu da ake kyautata zaton abin fashewa ne a harabar wani masallaci da ke unguwar Abuja Sheraton a Maiduguri.

Ya ce, “Wannan labari ba shi da tushe balle makama, domin babu wani abin fashewa da jami’an tsaro suka samu wanda zai zama barazana ga zaman lafiyar al’umma.”

Hakazalika, ya yi gargaɗin cewa, “Yaɗa bayanai marasa tushe na iya sanya mazauna birnin Maiduguri cikin firgici tare da kawo cikas ga ƙoƙarin hukumomin tsaro na tabbatar da zaman lafiya a tsakanin al’umma.”

A cewarsa, “Ya kamata jama’a su riƙa tabbatar da sahihancin labarai daga amintattun majiyoyi kafin su yaɗa su a kafofin sadarwar zamani.”

Shi ma Malam Bukar Abubakar ya ce, “Akwai buƙatar jama’a su tsaftace yadda suke amfani da kafofin sadarwa domin kauce wa haddasa husuma a cikin al’umma.”

Wasu mazauna birnin, ciki har da Mathew Joshua da Ahmed Mahmud, sun ce, “Duk da matsalolin tsaro da ke addabar wasu sassan jihar, akwai buƙatar jama’a su kwantar da hankalinsu tare da gujewa yaɗa rahotannin da ba a tabbatar da su ba, waɗanda ka iya ƙara dagula zaman lafiya a Maiduguri.”

Afrika, Labarai, Najeriya, Tsaro

Post navigation

Previous Post: Gwamnatin Trump Tana Cigaba Da Korar Baki Daga Amurka
Next Post: Yunkurin Samar Da ‘Yan Sandan Jihohi Na Kara Kankama A Najeriya

Karin Labarai Masu Alaka

Shugaba Trump Yace Babu Maganar Kawo Karshen Yakin Amurka Da Iran Amurka
Hawan Durba A Fadar Sarkin Zazzau Afrika
Wike: Bazamuyi Sake Fubara Ya Sake Samun Nasara Ba Najeriya
Kakakin Majalisar Kasar Amurka Yana Tsaka Mai Wuya Game Da Kasafin Kudi Amurka
Dakarun Zaman Lafiya Na Majalisar Dinkin Duniya Sun Rasa Rayukan Su Afrika
Sojojin Isra’ila Sun Kashe Babban Kwamandan Kungiyar Hezbollah Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Alejandro Balde Na Dab Da Komawa Manchester United Daga Barcelona
  • Kocin Newcastle Matthias Ya Ce Lewis Hall Ba Zai Koma Manchester United Ba
  • Dan Wasan Baya Na Chelsea, Disasi, Zai Yi Gwajin Lafiyarsa A Crystal Palace
  • Gwamnan Gombe Ya Taya Sarkin Musulmi Murnar Cika Shekaru 70, Ya Yi Masa Addu’ar Ƙarin Lafiya Da Tsawon Rai
  • Magoya Bayan Liverpool Sun Bukaci Iraola Ya Ɗauki Mataki Mai Tsauri Kan Szoboszlai

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Dalibin Jami’a Ya Rasa Ransa A Birnin Dakar Yayin Zanga Zanga Afrika
  • ‘Yan Bindiga Sun Kashe Dan Gaddafi A Gidansa Dake Kasar Libya Afrika
  • Magoya Bayan Nice Sun Kai Hari Wa ‘Yan Wasansu Wasanni
  • Hukumomin Tsaron Kenya Sunce ‘Yan Kasar Suna Fafata Yaki Da Dakarun Rasha A Ukraine Afrika
  • Tinubu Ya Lashe Zaɓen Fidda Gwanin APC Da Kuri’u Miliyan 11 Afrika
  • Sojojin Amurka Sunfara Isowa Gabas Ta Tsakiya Amurka
  • Kungiyoyi Sunyi Hasashen Jinkiri A Bunkasar Tattalin Arzikin Kashen Afirka Afrika
  • Gwamna Abba Kabir Ya Zabi Garo A Matsayin Mataimaki Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.