Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Amurka Tayi Barazanar Zata Rage Tallafin Da Take BayarwaSudan Ta Kudu, Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Farashin Mai Ya Fadi Fiye Da Dala Daya Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Sojojin Najeriya Sun Kashe Fitaccen ’Yan Bindiga Kallamu A Jihar Sakkwato Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya Da Kasar Saudiya Sun Kulla Yarjejeniyar Tsaro Labarai
  • Gwamna Fubara Ya Koma Jam’iyar APC Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

An Kai Hari Da Jirgi Mara Matuki A Kusa Da Matatar Mai Din Kasar Sundan
Published: December 11, 2025 at 9:36 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

An kashe wasu mutane da dama a harin da aka kai da maraicen talata da jirgin saman drone a kusa da matatar mai mafi girma a kasar Sudan.

Rundunar sojojin wucin gadi ta RSF, wadda tun shekarar 2023 take gwabza yaki da rundunar sojojin kasar ta Sudan, ta ce sojojin gwamnati ne suka kai hari kan matatar dake Heglig, kwana guda a bayan da dakarun RSF suka kwace wannan matata dake kusa da bakin iyakar kasar da Sudan ta Kudu.

Dukkan sassan biyu sun fada ma kamfanin dillancin labarai na Associated Press cewa ba su da cikakken adadin wadanda aka kashe ko aka ji ma rauni, amma kafofin labarai a yankin sun ce an kashe shugabanni 7 na wasu kabilu tare da sojojin rundunar RSF

Rundunar RSF ta kuma ce akwai sojojin Sudan ta Kudu a wannan harin da ta ce ya saba dokoki na kasa da kasa.

Rundunar sojojin Sudan ta tabbatar da kai hari da jiragen drone wadanda ta ce an auna su ne a kan mayakan rundunar RSF.

Gwamnatin jihar Unity ta Sudan ta Kudu ta tabbatar da kashe sojoji uku na Sudan ta Kudu.

Afrika

Post navigation

Previous Post: NNPC Da Wasu Kamfanoni Sunyi Yarjejeniyar Iskar Gas
Next Post: Kasar Iceland Ta Kauracewa Bikin Gasar Wakokin Shekara Mai Zuwa

Karin Labarai Masu Alaka

Muna Kira Ga Kasashen Duniya Su Sa Baki Don A Saki Mohamed Bazoum Afrika
An Damke Matasa Masu Gurza Kudaden Ketare Na Jabu Afrika
Gwamnatin Soji A Nijar Ta Hana Fitar Da Albarkatun Kasa Afrika
Shugaban Guinea-Bissau Umaro Na Fuskantar Matsin Lamba Afrika
Kasar Belarus Zata Taffawa Jamhuriyar Nijar Afrika
Amurka Na Shirin Kauracewa Taron Kungiyar Kasashen G20 Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Ministan Tsaro Ya Umarci Janye Sojoji Daga Shingayen Bincike a Tituna
  • Atiku Ya Zargi Gwamnati Da Kama ‘Yan Adawa
  • Rashin Tsaro: Gwamnati Ta Bada Umarnin Daukar Ma’aikata Sama Da 94,000
  • Najeriya Ta Gabatar Da Tayin Karbar Bakuncin Wasannin Afirka Na 2031.
  • Mulkin Kama Karya Yazo Karshe a Kasar Bulgaria

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Rediyo
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • Jakadan Kasar Sin a Najeriya Ya Ziyarci Tinubu Najeriya
  • Kyaftin Na Super Eagles Ya Yi Ritaya. Wasanni
  • Mun Kwato Kimanin Naira Biliyan 40 Na Badakala A Tsawon Shekara Daya Labarai
  • Eziekel Gomos Ya Zamo Babban Daraktan Sakatariyar Zauren Gwamnonin Arewa Najeriya
  • ‘Yan Wasan Kwallon Kafar Najeriya A Shirye Suke Wasanni
  • Amurka Ta Nuna Damuwa Kan Matsalar ‘Yan Gudun Hijira A Najeriya Najeriya
  • Akwai Bukatar Bincikar Umurnin Da Sakataren Tsaro Pete Ya Bada Amurka
  • Gwamna Fubara Ya Koma Jam’iyar APC Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.