Babban sakataren MDD, Antonio Guterres, yace akwai babban kuskure kan yadda Isra’ila ta gudanar da farmakin soja a zirin Gaza, kuma akwai kwakkwarar shaidar cewa ta aikata laifuffukan yaki a lokacin hare-haren.
Da yake magana yau laraba a wajen wani taron da kamfanin dillancin labarai na Reuters ke shiryawa, Mr. Guterres yace an yi biris baki daya da illar hare-haren a kan fararen hula da kuma lalata muhallansu a fadin Gaza.
Yace Isra’ila ta ce manufarta ita ce ta murkushe Hamas, amma kuma, ba Hamas din aka murkushe ba.
An kashe mutane fiye da dubu 70 a Gaza a lokacin wannan farmaki na Isra’ila, wanda ya biyo bayan harin da Hamas ta kai ta kashe mutane 1200 tare da kama mutane 251 a watan Oktobar 2023.
Da aka tambaye shi ko akwai alamun an aikata laifuffukan yaki a wannan farmaki na Isra’ila, babban sakataren na MDD yace akwai kwararan dalilai na yarda da cewa an aikata hakan.
An kulla yarjejeniyar tsagaita wuta a yankin tun 10 ga watan Oktoba, amma Isra’ila ta ci gaba da kai hare-hare tare da rushe gine-ginen da take ikirarin cewa cibiyoyin Hamas ne.


