Mataimakin shugaban majalisar dattawan Najeriya, Barau Jibrin, ya karyata zargin cewa majalisar dokoki ta ƙasa tana bin umarnin bangaren zartarwa ba tare da ‘yanci ba.
Barau Jibrin ya bayyana hakan ne a Ilorin yayin da yake gabatar da laccar bikin yaye ɗalibai karo na 15 a Jami’ar Al-Hikmah, inda ya ce haɗin kai tsakanin majalisa da bangaren zartarwa an yi shi ne domin samar da kyakkyawan shugabanci.
Ya danganta kyakkyawar alaƙar da ke tsakanin bangarorin biyu da kwarewar Shugaba Bola Tinubu a matsayin tsohon gwamna kuma ɗan majalisa, yana mai cewa hakan ya ƙarfafa fahimta, sadarwa da shawarwari, musamman wajen gabatar da kudurorin dokoki.
Mataimakin shugaban majalisar dattawan ya ce wasu na kuskuren fassara wannan haɗin kai a matsayin majalisa ta zama “yar amshin shata” kawai, yana mai jaddada cewa haɗin kai ya fi rikici amfani ga ci gaban ƙasa.
Ya ƙara da cewa dorewar dimokuraɗiyya na buƙatar bin kundin tsarin mulki, hikima da wayayyun ‘yan ƙasa masu kishin ƙasa.


