Sarkin Kagarko Ya Rasu Yana Da Shekaru 110
Allah Ya yi wa Mai Martaba Sarkin Kagarko Alhaji Sa’ad Abubakar rasuwa a yau Alhamis. Ya rasu yana mai shekara 110. Za a gudanar da jana’izar sa a gobe Juma’a bayan Sallar Juma’ah a Masallacin kofar Fadar sa dake Kagarko, jihar Kaduna a Najeriya. Basaraken Ya Rasu bayan fama jinya a Wani asibiti a Kaduna.

