Daya daga cikin ‘Yan Jarida 13 da sukayi hatsarin Mota a Bauchi ya Rasuwa
Allah ya karbi rayuwar daya daga cikin ‘Yan Jarida da sukayi hatsarin Mota a Jihar Bauchi da ke Arewa maso gabas a Najeriya mai suna Khani Ben.
Khani Ben ma’aikacin ne a gidan talabijin na Channels TV ya shahara ta wajan daukar hoto kuma yana wakiltar tashar Channels TV a gidan Gwamnatin Jihar Bauchi.
A ranar Juma’a 6 ga watan Fafurairun 2026 ne tawagar ‘yan Jarida a jihar Bauchi sukayi wani mumunar hatsarin Mota a kan hanyar Yashi zuwa Yelwan Duguri,yayin da zasuje aikin Kaddamar da katafaren Makaranta a garin Yelwan Duguri dake Karamar hukumar Alkaleri a Bauchi wacce hukumar raya Arewa maso gabas ( NEDC) ta gina.
Ben yana daya daga cikin mutane 14 da hatsarin ya rutsa da su
Tun bayan faruwar lamarin Ben ya samu kansa cikin mawuyacin hali ganin yana daya daga cikin wadda suka fi samun mumunar rauni sai dai dukkanin su sun samu kulawa daga Gwamnatin Jihar Bauchi da (NEDC) a Babban Asibitin kuyarwa na Jami’ar Abubakar Tafawa Balewa da ke Bauchi inda anan ne rai yayi halinsa.
Rasuwar Mr Ben ya bar babbar gibi a harkar jarida musamman a kafar watsa labari ta Channels TV da ma gidan Gwamnatin Jihar Bauchi inda yake aiki da kuma abokan aikinsa da sauran ma’abota gidan talabijin na Channel TV.
Mr Khani Ben ya kasance haziki kuma jajurtatce wajan aikin jarida da kuma iya mu’amula da al’uma ya rasu ya bar matarsa da ‘ya’yansa biyu.
“Muna mika ta’aziya wa Iyalai, da ‘yan uwansa da hukumar gudanawa na Channels TV da ‘yan Jaridar jihar Bauchi tare da Gwamnatin Jihar Bauchi bisa wannan Babban rashi. GTA Hausa.


