Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Amurka Tayi Barazanar Zata Rage Tallafin Da Take BayarwaSudan Ta Kudu, Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Farashin Mai Ya Fadi Fiye Da Dala Daya Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Sojojin Najeriya Sun Kashe Fitaccen ’Yan Bindiga Kallamu A Jihar Sakkwato Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya Da Kasar Saudiya Sun Kulla Yarjejeniyar Tsaro Labarai
  • Gwamna Fubara Ya Koma Jam’iyar APC Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

ECOWAS Zata Taimakawa Kasar Benin Da Dakarun Soji
Published: December 7, 2025 at 3:30 PM | By: Aliyu Bala Gerengi | Updated: December 7, 2025

Ƙungiyar raya tattalin arzikin ƙasashen Afirka ta Yamma Ecowas ta ce a shirye take ta taimaka wa Jamhuriyar Benin da sojoji domin daƙile juyin mulkin da wasu sojoji suka yi iƙirarin yi.

Matakin na Ecowas na zuwa ne bayan wani rukunin soji sun sanar da kifar da gwamnatin Shugaba Patrice Talon a kafar talabijin ɗin ƙasar a ranar Lahadi tare da kafa gwamnatin riƙon ƙwarya.

Wata sanarwa da ƙungiyar ta fitar ta ce ta ɗora wa sojojin alhakin “duk wani rai da aka rasa” sakamakon yunƙurin nasu.

“Ecowas za ta taimaka wa gwamnati da al’umma da duk abin da ya kamata, ciki har da aika dakarun ko ta kwana domin kare tsarin mulki da kuma ‘yancin Benin,” a cewar sanarwar da hukumar Ecowas mai hedikwata a Abuja ta fitar

Sai dai hukumomi a ƙasar sun ce sun shawo kan lamurra bayan yunƙurin juyin mulkin.

“An shawo kan lamarin sannan mafi yawan rundunar soja na goya wa shugaban ƙasa baya haja kuma muna ƙara shawo kan al’amuran.” kamar yadda Ministan harkokin waje Shegun Adjadi Bakari ya faɗa wa kamfanin labarai na Reuters.

Afrika

Post navigation

Previous Post: An Murkushe Wani Yunkurin Juyin Mulki A Jamhuriyar Benin
Next Post: ‘Yan Ta’adda Sun Hallaka Malaman Makaranta A Tilabery

Karin Labarai Masu Alaka

Da Arzikin Mu: Bamu Ba Bautawa Turawan Yamma Afrika
Jiragen Saman Yakin Najeriya Suka Gurgunta Yunkurin Juyin Mulki A Benin Afrika
An Damke Matasa Masu Gurza Kudaden Ketare Na Jabu Afrika
Amurka Na Shirin Kauracewa Taron Kungiyar Kasashen G20 Afrika
Muna Kira Ga Kasashen Duniya Su Sa Baki Don A Saki Mohamed Bazoum Afrika
Nijar: Zamu Tsananta Bincike A Bakin Iyakokin Mu Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Shirin Manuniya Yau Juma’a 12.12.2026
  • Ministan Tsaro Ya Umarci Janye Sojoji Daga Shingayen Bincike A Tituna
  • Atiku Ya Zargi Gwamnati Da Kama ‘Yan Adawa
  • Rashin Tsaro: Gwamnati Ta Bada Umarnin Daukar Ma’aikata Sama Da 94,000
  • Najeriya Ta Gabatar Da Tayin Karbar Bakoncin Wasannin Afirka Na 2031

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Rediyo
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • Marc Brys: “Eto’o Baiyi Adalci Ga Onana, Da Vincent, Ba” Wasanni
  • Shugaban Guinea-Bissau Umaro Na Fuskantar Matsin Lamba Afrika
  • Kanal Sani: Idan ‘Yan-Ta’adda Zasu Mutunta Sulhu To Gwamnati Ta Duba Hakan Labarai
  • Oliseh, Ya Ba Eric Chelle, Shawara Da Ya Zamo Mai Tsauri AFCON 2025. Wasanni
  • Mizanin Tattalin Arzikin Najeriya Na 2024 Ya Karu Da Kashi 3.84% Labarai
  • Samar Da Tsaro A Jihar Kano Ba Sai An Sa Siyasa Ba! Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnatin Tarayya Ta Samu Nasarar Ceto Wasu Daliban St. Mary’s Tsaro
  • An Damke Matasa Masu Gurza Kudaden Ketare Na Jabu Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.