Yayinda a yau Talata jami’iyyar APC a jihar Filato ke shirin karbar gwamnan jahar, Caleb Mutfwang, bayan ya chanza sheka daga jami’iyyar PDP, komitin shirye-shiryen karbar gwamnan yace matakin da gwamnan ya dauka domin hadin kan al’ummar jahar ne da samadda ci gaba.
A taron ganawa da manema labarai a Jos, fadar jaha Filato, shugaban komitin kuma tsohon mataimakin kakakin majalisar wakilai ta Najeriya, Ahmad Idris Wase yace chanza sheka da gwamnan jahar ta Filato yayi shine matakin farko na samun zaman lafiya da ci gaba a jahar da ta sha fama da rikita-rikita.
Gwamnan jahar Filato, Caleb Mutfwang ya sami gagarumin goyon bayan jama’ar jahar a karkashin jami’iyyar PDP, duk da jeka ka dawo da aka yi a kotuna daban-daban, bias cewa jami’iyyar PDP bata da tsari a matakin jaha, kafin zaben dubu biyu da ishirin da uku.
Honarabul Nuru Shehu shine tsohon mai ba gwamnan hajar Filato Caleb Mutfwang shawara a mazabar Jos ta Arewa, yace gwamnan bai nuna dattako ba.
Kafin komawar gwamnan na jahar Filato, Caleb Mutfwang zuwa jami’iyyar APC, an yi ta kai ruwa rana tsakanin ‘ya’yan jami’iyyar, wanda wadansu suka nuna basu kaunar shigansa jami’iyyar.
Alhaji Saleh Abdullahi Zazzaga na daga cikin wadanda suka tsaya kai da fata wajen ganin gwamnan ya tsallaka zuwa APCn yace irin ayyukan da gwamnan yayi shi yasa suka bukaci kasancewarsa a jami’iyya daya da shagaban kasa, ya kara da cewa sun riga sun bashi shugabancin jami’iyyar a jaha da ma tikitin shiga zaben gwamna a dubu biyu da ishirin da bakwai.
A zaben shekara ta dubu biyu da ishirin da uku dai gwamnan, Caleb Mutfwang ya yi fafata da shugaban jami’iyyar APC na yanzu, Farfesa Nentawe Yilwatda a takarar gwamna, wanda masu sharhi ke bada shawarar jira da kallon yadda siyasar jahar zata kasance nan gaba.
Ga Rahoton Zainab Babaji Daga Jos a Najeriya


