Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Najeriya Ta Mika Koke Ga FIFA Tana Zargin DR Congo Ta Sanya ‘Yan Wasan Da Basu Cancantaba Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • ‘Yan Tawayen M23 Masu Samun Goyon Bayan Rwanda Basu Jamye A Ulvira Ba Labarai
  • Afirka Ta Kudu Ta Kama ‘Yan ƙasar Kenya Su Bakwai Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • ‘Yan Bindiga Sun Kama Akalla Mutane 13 A Wani Coci A Jihar Kogi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Ahmed Musa, Yayi Ritaya A ƙwallon ƙasa Da ƙasa Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Gwamnatin Jihar Yobe: Ana Cin Zarafin Fursunoni A Gidan Gyaran Halin Potiskum
Published: December 17, 2025 at 11:29 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Gwamnatin jihar Yobe a arewa maso gabashin Najeriya ta tabbatar da samuwar wata ƙungiyar dake lalata tare da cin zarafin fursunoni a Gidan Gyaran Hali na Potiskum.

Mai bai wa Gwamna shawara kan harkokin tsaro, Birgediya Janar Abdulsalam Abubakar mai ritaya, ne ya bayyana hakan yayin da yake yi wa manema labarai bayani bayan taron Majalisar Tsaron Jihar da aka gudanar a ranar Talata a Damaturu.

Abdulsalam ya bayyana lamarin a matsayin babbar cin amana, inda ya ce ana zargin wasu jami’an gidan yari da yi wa wata fursuniya ciki a cikin gidan gyaran halin.

Ya ce hakan na nuna sakaci wajen aiki da kuma rashin kulawa yadda ya kamata, yana mai cewa a ka’ida babu yadda za a yi jami’in tsaro namiji ya shiga sashen mata idan ana sa ido yadda ya dace.

Mai ba da shawarar kan tsaro ya ce, bincike na ci gaba da gudana, inda ya kara da cewa har yanzu ba a tantance adadin jami’an da ke da hannu a lamarin ba, domin ana ci gaba da kama wasu da ake zargi inda ya kara da cewa, al’amarin wata ƙungiya ce mai faɗi, bawai mutum ɗaya ba, kuma akwai masu taimaka musu ciki har da wasu jami’an mata.

Sai dai Abdulsalam ya nuna fatan cewa duk wanda aka samu da laifi a binciken da Hedikwatar Hukumar Gyaran Hali ta Ƙasa ke gudanarwa, za a miƙa shi ga ‘yan sanda domin gurfanar da shi a gaban kotu.

Ya ƙara da cewa gwamnatin jihar ta riga ta kai ƙorafi ga shugabancin Hukumar Gyaran Hali ta Ƙasa da Ma’aikatar Harkokin Cikin gida yana mai jaddada cewa gwamnati na da alhakin kare rayuka, dukiya da mutuncin al’umma.

A game da samar da tsaro lokacin bukukuwan Kirsimeti, Kwamishinan ‘Yan Sandan Jihar, Emmanuel Ado, ya ce an shirya tsaro sosai, inda aka tura jami’ai da dama zuwa wuraren ibada da wuraren shakatawa.

Ya tabbatar wa mazauna jihar, musamman mabiya addinin Kirista, cewa za su gudanar da bukukuwansu cikin kwanciyar hankali ba tare da fargaba ba.

Tsaro

Post navigation

Previous Post: Kotu A Kasar Faransa Ta Daure Lumbala Shekaru 30 Bisa Laifin Cin Zarafi
Next Post: Gwamnatin Gombe Zata Inganta Samar Da Wuta Wajen Amfani Da Hasken Rana

Karin Labarai Masu Alaka

Sarkin Musulmi Yayi Magana Game Da Matsalar Tsaron Kasar Tsaro
Boko Haram Sun Dauke Kansiloli A Borno Tsaro
Shugaba Tinubu Ya Umarci Janye ‘Yan Sanda Masu Gadin Ministoci Tsaro
Kungiyar Kwadago Ta NLC Ta Gudanar Da Zanga-Zanga Bisa Matsalar Tsaro Tsaro
Gwamnatin Kano Ta Samar Da Wasu Dabarun Inganta Tsaro Tsaro
An Sace Masu Ibada A Wata Majami’ar Ecwa A Jihar Kogi Tsaro

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Fintiri: Zamu Maida Jihar Adamawa Sabuwar Duniya
  • Gwamnatin Najeriya Ta Dauki Matakai Don Farfaɗo Da Maɗaba’ar Gwamnati
  • Boko Haram Sun Dauke Kansiloli A Borno
  • A Kowacce Rana Kasar China Tana Sayan Danyen Mai Ganga Dubu 600 Daga Kasar Venezuela
  • Kotun Kasar Rasha Ta Daure Dan Kasar Belarus Shekarar 22 A Kurkuku

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • Malami: “Da Gwamnatin Tarayya Na Daukar Shawara Da Ba’a Kai Inda Ake Ba” Najeriya
  • Rundunan  ‘Yan Sandan Jihar Bauchi, Ta Miƙa Miyagun Ƙwayoyi Da Ta Kama Wa NDLEA. Labarai
  • Ministan Yaɗa Labarai: Ceto Daliban Neja An Samu Natsuwa A Kasa Labarai
  • Gidauniya: An Fara Tiyatar ‘Hernia’ Da ‘Hydrocele’ Kyauta A Jihar Katsina Labarai
  • ECOWAS Da AU Sun Nuna Damuwa Kan Juyin Mulki A Guinea-Bissau Afrika
  • An Saka Dokar Hana Fita A Karamar Hukumar Lamurde Jihar Adamawa Tsaro
  • Shugaba Tinubu Ya Umurci Janyewa Manyan Mutane ‘Yan Sanda Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Majalisar Dattawa Ta Wanke Janar Christopher Musa A Matsayin Minista Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.