Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Zelensky: Gabas Ta Tsakiya Na Iya Nuna Makomarmu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Mojtaba Khamenei Ya Zama Sabon Jagoran Jamhuriyar Musulunci ta Iran Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnatin Najeriya Taja Hankalin ‘Yan Najeriya Mazauna Iran Da Kasashen Larabawa Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnan Gombe Yace An Sace Yara 48 A Jihar Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • ‘Yan Bindiga Suna Cigaba Da Kashe Mutane A Garin Gwana Dake Jihar Bauchi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Hadakar Gwamnatin Najeriya Da Amurka Ne Suka Kai Hari Sokoto
Published: December 26, 2025 at 9:50 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Gwamnatin Najeriya ta sanar da nasarar kai hare-haren da aka tsara cikin tsanaki kan wasu manyan sansanonin ’yan ta’addan ISIS guda biyu da ke cikin dajin Bauni, a ƙaramar hukumar Tangaza ta Jihar Sokoto.

A cewar sanarwar da Ma’aikatar Yaɗa Labarai da Wayar da Kai ta fitar, an gudanar da harin ne tare da haɗin gwiwa tsakanin Najeriya da Ƙasar Amurka, bayan bayanan sirri sun tabbatar da cewa ’yan ISIS daga yankin Sahel na amfani da wuraren a matsayin wajen taro da shiryawa domin kai manyan hare-haren ta’addanci a cikin ƙasar nan, tare da taimakon wasu ƙungiyoyin t’addanci na cikin gida.

Sanarwar ta ce an kai hare-haren ne tsakanin ƙarfe 12:12 na dare zuwa 1:30 na safiyar Juma’a, 26 ga Disamba, 2025, bayan samun cikakken amincewar Shugaban Ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, GCFR.

An bayyana cewa an gudanar da aikin ne a karkashin tsayayyen tsarin umarni da jagoranci, tare da shigar Rundunar Sojin Najeriya, a ƙarƙashin kulawar Ministan Tsaro, Ministan Harkokin Waje, da Babban Hafsan Tsaro.

Hare-haren sun samo asali ne daga tashar jiragen ruwa da ke yankin Tekun Guinea, bayan dogon nazarin bayanan sirri, shirye-shiryen aiki da bincike na sama.

Jimillar harsasai masu bin tsarin GPS guda 16 ne aka yi amfani da su ta hanyar jiragen sama marasa matuƙa samfurin MQ-9 Reaper, lamarin da ya kai ga kawar da ’yan ISIS ɗin da ke ƙoƙarin shigowa Najeriya ta hanyar yankin Sahel.

Sai dai a yayin aikin, wasu ragowar harsasai sun faɗo a yankin Jabo da ke Ƙaramar Hukumar Tambuwal ta jihar Sokoto, da kuma a Offa ta Jihar Kwara, kusa da wani otel.

Gwamnati ta tabbatar da cewa babu wani farar hula da ya jikkata a wuraren, kuma jami’an tsaro sun gaggauta killace yankunan.

Gwamnatin Tarayya ta jaddada aniyarta ta ci gaba da kawar da duk wata barazanar ta’addanci, musamman daga ƙungiyoyin ta’addanci na ƙetare da ke ƙoƙarin tauye ikon Najeriya da tsaron al’ummarta.

Sanarwar ta ƙara da cewa Najeriya na ci gaba da aiki kafaɗa da kafaɗa da ƙawayenta na dabarun tsaro da abokan hulɗa domin tabbatar da zaman lafiya mai ɗorewa, tsaron iyakoki da kwanciyar hankali a yankin.

Gwamnati ta tabbatar wa ’yan Najeriya cewa tana da cikakken iko kan tsarin tsaron ƙasa, tare da ƙudirin kare rayuka da dukiyoyin jama’a, sannan kuma an buƙaci al’umma da su kasance cikin kwanciyar hankali da taka-tsantsan yayin da ake ci gaba da ɗaukar matakan murƙushe duk wata ƙungiyar ta’addanci da ke barazana ga ƙasa.

Najeriya

Post navigation

Previous Post: Ankara Gano Wani Abu Mai Kama Da Abun Fashewa A Jabo Jihar Sokoto
Next Post: Gwamnatin Tarayya Ta Bayyana Hadakar Ta Da Amurka Wajen Yakar ‘Yan Ta’adda

Karin Labarai Masu Alaka

‘Yan Bindiga Sun Kashe Fiye Da Mutane 50 Tare Da Sace Mata Da Yara A Jihar Zamfara Najeriya
Jagoran Addinin Kirista A Kaduna Ya Rabawa Fiye Da Musulmai Dubu Kayan Abincin Azumi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Wata Tankar Mai Ta Kife A Apapa Legas Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Fitaccen Dan Jarida a Sokoto Surajo Dalhatu Sifawa Ya Rasu Najeriya
Gwamnatin Sokoto Tabada Umarnin Biyan Albashin Watan Fabrairu Labarai
Shugaba Tinubu Yakarawa Mambobin ASUU Kashi 40 Na Albashi Najeriya

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • ‘Yan Uwa Musulmi A Jihar Gombe Sunyi Allah Wadai Da Kisan Ayatollah Khomeini
  • An Samu Kaburbura Biyu Dauke Da Gawarwaki 173 A Kasar Kwango
  • Yan Bindiga Suna Cigaba Da Kashe Mutane A Garin Gwana Dake Jihar Bauchi
  • Karancin Iskar Gas Kalubale Ne Ga Wutar Lantarki
  • Zelensky: Gabas Ta Tsakiya Na Iya Nuna Makomarmu

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • Akwai Yiwuwar Iran Da Amurka Su Cimma Matsayar Dakatar Da Shirin Nukiliya Amurka
  • Amurka Da Iran Zasu Tattauna A Kasar Oman Amurka
  • Ghana Ta Haramta Hakar Ma’adinai A Gandunan Dajin Data Kebe, Labarai
  • Kamfanin Hakar Ma’adanai Na Kasar Kanada Ya Cigaban Da Aikinsa Labarai
  • Zelensky Na Buƙatar Ganawa Da Trump Domin Cimma Matsaya Kan Batutuwa Masu Sarƙaƙiya Labarai
  • Jakadan Kasar Sin a Najeriya Ya Ziyarci Tinubu Najeriya
  • Kotun Daukaka Kara A Faransa Zata Tabbatar Da Hukuncin ‘Yan Jam’iyyar Ra’ayin Rikau Labarai
  • An Bude Kamfanin Sarrafa Ma’adanai A Kasar Mozambique Labarai
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.