Babban Hafsan Sojin Ƙasa na Najeriya, Laftanar-Janar Shaibu ya yaba, ya ce buɗe sabbin cibiyoyin horas da kuratan sojoji a jihohin Kudu zai ƙara ƙarfin rundunar wajen daukar dakaru a faɗin ƙasar.
Laftanar-Janar Shaibu ya tuna cewa Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu ya sahale buɗe sabuwar cibiyar horas da sabbin kuratan sojojin ne a Abakaliki da ke Jihar Ebonyi.
Ya kara da cewa a mako mai zuwa Depot na Abakalaki da kuma na Osogbo da ke Jihar Osun za su yaye sabbin kuratan sojoji da suka kammala horaswa.
Ya bayyana haka ne a yayin bikin yaye sabbin dakarun soji 3,439 da aka yi a Cibiyar Horas da Sabbin Kuratan sojoji da ke Zariya, inda ya shawarce su da su zama masu kishin ƙasa da jajircewa.
Ya taya sabbin sojojin murnar kammala horon farko na soja, wanda ya ce, shi ne matakin farko na doguwar tafiyar sadaukarwa, kishin ƙasa, da hidima ga al’umma.
A karshe, Laftanar-Janar Shaibu ya bayyana ranar a matsayin ranar nuni da babban ci gaba wajen cika manufar rundunar sojojin Najeriya ta faɗaɗa karfin ma’aikata.


