ICPC ta gayyaci Dangote kan zargin biyan kuɗin makaranta dala miliyan $7 ga tsohon shugaban NMDPRA.
Hukumar Yaƙi da Cin Hanci da Rashawa ta Ƙasa (ICPC) ta gayyaci ɗan kasuwa Aliko Dangote domin ya ba da ƙarin bayani kan ƙorafin da ya shigar kan tsohon Darakta Janar na Hukumar Kula da Harkokin Man Fetur ta Ƙasa (NMDPRA), Alhaji Farouk Ahmed.
Ana sa ran Dangote zai bayyana da kansa ko kuma ya turo lauyansa, Ogwu Onoja (SAN), ranar litinin yayin da ICPC za ta fara binciken ƙorafin a hukumance.

Rahotanni sun ce hukumar ta kafa wani kwamitin manyan masu bincike a ranar Juma’a domin gudanar da binciken, kuma ta bukaci Dangote ya gabatar da dukkan hujjojin da ke hannunsa ga hukumar yaƙi da cin hanci.
Dangote ya zargi Farouk da cin hanci da almundahana, ciki har da kashe miliyoyin daloli wajen karatun ‘ya’yansa huɗu a makarantu masu tsada da ke Switzerland.
Har ila yau, ɗan kasuwar ya zargi Farouk da yin zagon kasa ga tattalin arziki wajen raunana tace man fetur a cikin gida, ta hanyar haɗa baki da ‘yan kasuwar waje da masu shigo da mai, da ya ci gaba da ba su lasisin shigo da main fetur.


