Rundunar ‘Yan Sanda ta Jihar Gombe na sanar da daukacin jama’a cewa, bayan wani muhimmin taron tsaro da aka gudanar tare da sauran hukumomin tsaro da masu ruwa da tsaki, an yi cikakken nazari kan halin tsaro da ake ciki a jihar.
Sanarwar Jami’in hulda da jama’a na Rundunar DSP Buhari Abdullahi ta bayyana cewa, Bayan tattaunawa mai zurfi da kuma nazari kan matsalolin tsaro da ke akwai, an cimma matsaya cewa za a ci gaba da aiwatar da takaita amfani da babura a cikin birnin Gombe. Wannan takaita zai ci gaba da aiki daga karfe 7:00 na yamma zuwa 6:00 na safe a kowace rana, kuma za a fara sake aiwatar da shi daga ranar Juma’a, 3 ga Afrilu, 2026.
An dauki wannan mataki ne domin hana amfani da babura wajen aikata laifuka da kuma kara inganta tsaro da kare rayuka da dukiyoyin jama’a a fadin jihar.
Rundunar na godiya da hadin kai da fahimtar da jama’a masu bin doka suke nunawa, tare da kira ga kowa da kowa da ya bi wannan umarni domin tabbatar da tsaro da zaman lafiya.
Haka kuma, ana karfafa gwiwar jama’a da su kasance masu lura tare da kai rahoton duk wani motsi ko aiki mai tayar da shakku ga ofishin ‘yan sanda mafi kusa da su.
Rundunar ‘Yan Sanda ta Jihar Gombe na ci gaba da jajircewa wajen kare rayuka da dukiyoyin jama’a a fadin jihar.
Za a ci gaba da sanar da jama’a duk wani sabon ci gaba dangane da wannan batu.


