Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Najeriya Ta Dauki Hayan Amurkawa Don Kyautata Alaka Da Trump Game Da Kisan Kiristoci Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnatin Tarayya Ta Cimma Yarjejeniya Da Kungiyar Malaman Jami’oi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Amurka Ta Baiwa Najeriya Wasu Muhimman Kayan Yaki Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Trump Yayi Kira Ga ‘Yan Ƙasar Iran Su Ci Gaba Da Zanga Zanga Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Syria: Mutane Sun Yi Zanga Zanga Domin Nuna Rashin Amincewa Da Korar Kurdawa A Birnin Aleppo Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Isra’ila Zata Karbi Mutanenta A Yankin Gaza
Published: December 29, 2025 at 10:34 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Ana samun karin kasashen dake fitowa suna yin Allah wadarai da amincewar da kasar Isra’ila ta yi da yankin Somaliland na kasar Somaliya a zaman kasa mai ‘yanci.

Ba a san dalilin da ya sa isra’ila ta fito ranar Jumma’a tana fadin cewa ta amince da Somaliland a zaman ‘yan tacciyar kasa ba, amma kuma a farkon shekarar nan jami’an Amurka da na Isra’ila sun fada ma kamfanin dillancin labarai na Associated Press cewa Isra’ila ta tuntubi jami’an yankin na Somaliland, a kan ko zasu karbi Falasdinawa na yankin Gaza, a wani bangare na shirin Shugaba Trump a wancan lokaci na sake tsugunar da mutanen Gaza a wani wuri kuma tuni dai Amurka ta yi watsi da wancan shirin nata.

Wata sanarwar hadin guiwar da kasashe fiye da 20 tare da kungiyar kasashen Musulmi ta duniya OIC suka bayar ta yi watsi da wannan amincewa da isra’ila ta ce ta yi da yankin na Somaliland a zaman kasa mai cin gashin kai, ganin irin yadda hakan zai yi mummunar barazana ga zaman lafiya da kwanciyar hankali a yankin.

Yankin Somaliland ya bayyana ballewa daga Somaliya tun shekarar 1991, amma duk da cewa yana da gwamnati da takardar kudin sa daban, babu wata kasa a duniya da ta taba yarda da shi a zaman kasa.

Sanarwar kasashen ta kuma nuna rashin yarda ko miskala zarratin, da duk wani matakin da Isra’ila zata ce zata dauka dangane da wannan, wajen korar Falasdinawa karfi da yaji daga gidaje da garuruwa da yankunan su.

Ita ma kasar Sham, ko Syria, tayi tur da wannan mataki na Isra’ila a wata sanarwa dabam da ta bayar.

A ranar asabar, ma’aikatar harkokin wajen Amurka ta fitar da sanarwa tana jaddada ci gaba da mutunta kasar Somaliya wadda yankinta ya hada da yankin na Somaliland.

Gwamnatin tarayyar Somaliya ta fito ran jumma’a da kakkausar harshe tana yin tur da wannan matakin na Isra’ila da ta ce haramun ne.

Shi ma shugaban Kungiyar Tarayyar Kasashen Afirka, Mahmoud Ali Youssouf, yace duk wani matakin gurgunta diyaucin Somaliya na iya haddasa fitina a nahiyar.

Labarai

Post navigation

Previous Post: Anfara Kirga Kuri’a A zaben Kasar Guinea
Next Post: Ana Cigaba Da Tattaunawa Tsakanin Trump Da Zelensky Domin Tsagaita Wuta A Ukraine

Karin Labarai Masu Alaka

Tsohon Shugaban Brazil Bolsanaro Zai Tafi Gidan Yari Labarai
Rasha Na Cigaba Da Kai Hare-Haren Makamai Masu Linzami Ga Ukrain Labarai
Wasu Muhimman Abubuwa Da Najeriya Ba Zata Manta Da Su Ba A 2025 Labarai
Trump Yace Amurka Ta Kai Hare-Hare Masu Yawa Akan ‘Yan Ta’adda A Najeriya Amurka
Shugaban Ƙasar Koriya Ta Arewa Ya Halarci Gwajin Makami Mai Linzamin Kasar Labarai
China Ta Dawo Da Harajin Magungunan Hana Haihuwa Labarai

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Najeriya Ta Dauki Hayan Amurkawa Don Kyautata Alaka Da Trump Game Da Kisan Kiristoci
  • Gwamnatin Tarayya Ta Cimma Yarjejeniya Da Kungiyar Malaman Jami’oi
  • Kabiru Vice: Najeriya Zata Iya Nasara A Kan Moroko AFCON 2025.
  • Motar Yashi Ta Kashe Mutane Shida A Wani Coci Dake Legas
  • An Kaddamar Da Rijistar Zamani Ta Zamowa Mamba A Jam’iyar APC

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • An Samu Nasarar Karbo Karin Yara 130 Daga Hannun ‘Yan-Ta’adda Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • ‘Yan-Ta’adda Sun Yi Ma Wasu Mutane Yankan Rago A Jihar Neja Labarai
  • Abun Da Kuke Buƙatar Sani Game Da Gasar Cin Kofin Ƙasashen Afirka 2025 Wasanni
  • An Kai Hari Da Jirgi Mara Matuki A Kusa Da Matatar Mai Din Kasar Sundan Afrika
  • Kasashen Cambvodia Da Thailand Sun Kulla Yarjejeniyar Tsagaita Wuta Tsaro
  • Jagoran Kasar Iran Yace Basa Bukatar Tallafin Kasar Amurka Afrika
  • Shugaba Tinubu Ya Gabatar da Kasafin Kuɗin 2026 Najeriya
  • Sojin Najeriya Sun Hallaka ‘Yan Bindiga A Kano Da Katsina Tsaro
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.