Jamhuriyar Dimokuraɗiyyar Kongo ta sanar cewa za ta karɓi ‘yan ƙasashen waje da Amurka ke korar su daga ƙasar, ƙarƙashin wata sabuwar yarjejeniya da gwamnatin Donald Trump, kamar yadda gwamnati a Kinshasa ta bayyana a cikin wata sanarwa jiya Lahadi.
Gwamnatin ta ce za ta fara karɓar waɗanda aka kora daga watan Afrilu, amma ba ta bayyana adadin mutanen da ta amince za ta karɓa ba.
Sanarwar ta ƙara da cewa Amurka ce za ta ɗauki nauyin wannan shiri gaba ɗaya, ba tare da wani kuɗi daga gwamnatin Kongo ba. Haka kuma, an tanadi wuraren zama kusa da babban birnin ƙasar, wato Kinshasa, domin sauƙaƙa wa waɗanda za a kawo masauki.
Amurka ta riga ta tura wasu ‘yan ƙasashen waje da aka kora zuwa wasu ƙasashen Afirka da suka haɗa da Ghana, Cameroon, Equatorial Guinea da Eswatini, lamarin da ya janyo suka daga masana harkokin doka da kuma ƙungiyoyin kare haƙƙin ɗan Adam.
Wannan yarjejeniya na zuwa ne a daidai lokacin da gwamnatin Trump ke ƙoƙarin aiwatar da yarjejeniyar zaman lafiya tsakanin Kongo da Rwanda, tare da wata yarjejeniya da ke tabbatar da samun damar Amurka ga muhimman ma’adanan Kongo.


