Harin da jirgin mara matuki da ya kashe kakakin rundunar M23 Willy Ngoma a gabashin Kongo cikin wannan mako ya yi sanadin mutuwar akalla mutane tara, amma bai samu nasara kan kwamandan sojojin na ‘yan tawayen, wanda ya tsira da ransa, kamar yadda wasu majiyoyi hudu suka shaida wa kamfanin dillancin labarai na Reuters.
Harin ya afku ne a kusa da Rubaya, cibiyar hakar ma’adinan da ‘uan tawayen M23 ke kula da ita, wadda ke samar da kusan kashi 15% na albarkatun da ake samarwa a duniya, kuma a kwanan baya an saka shi cikin jerin sunayen kadarorin hakar ma’adinai da gwamnatin Kongo ta bai wa Amurka karkashin tsarin hadin gwiwar ma’adinai.
Mutuwar Ngoma dai na nuni da yadda rikicin ke ci gaba da ruruwa, inda ya kawar da daya daga cikin jiga-jigan ‘yan kungiyar ta M23, yayin da fadan ke kara kamari, duk kuwa da kokarin da masu shiga tsakani ciki har da Qatar suka yi na tsagaita wuta.


