Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Najeriya Ta Dauki Hayan Amurkawa Don Kyautata Alaka Da Trump Game Da Kisan Kiristoci Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnatin Tarayya Ta Cimma Yarjejeniya Da Kungiyar Malaman Jami’oi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Amurka Ta Baiwa Najeriya Wasu Muhimman Kayan Yaki Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Trump Yayi Kira Ga ‘Yan Ƙasar Iran Su Ci Gaba Da Zanga Zanga Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Syria: Mutane Sun Yi Zanga Zanga Domin Nuna Rashin Amincewa Da Korar Kurdawa A Birnin Aleppo Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Mali Da Burkina Faso Za Su Haramta Wa Amurkawa Izinin Shiga Ƙasashen Su
Published: January 1, 2026 at 10:44 AM | By: Bala Hassan

Kasashen Mali da Burkina Faso sunce za su hana Amurkawa izinin shiga kasashen su, martani kan irin wannnan matakai da gwamnatin Trump ta bada sanarwa akai a farkon watan Disemban 2025.

A cikin sanarwar da ma’aikatun harkokin kasashen wajen biyu suka bayar daban-daban a daren  litinin, kasashen biyu da suke Afirka ta yamma sunce suna daukar wannan matakine a zaman “martani” bayanda fadar White House ta bada sanarwar ranar 16 ga watan disemba cewa shugaban Amurka Donald Trump, zai kara kasashen su da wasu biyar a jerin kasashen da Amurka zata iya haramtawa shiga kasar.

Fadar White House tace jerin kasashen da matakin zai shafa zai fara aiki daga  1 ga watan Janairu na sabuwar shekara, ya shafi kasashe da suka ci gaba nuna rashin tantan-cewa na kwarai, yin kididdiga, da kuma musayar bayanai domin kare Amurka ta fuskar tsaro da kuma barazana kan zaman lafiya.

Mali ta fada a talata cewa shawarar da hukumomi a Washington suka dauka na sanya kasar cikin jerin kasashen da zata haramtawa shiga, ta yi hakan ne ba taredaa wata tuntuba ba, kuma hujjar data bayar na yin haka yayi karo da hakikanin al’amura.

Kasashen Mali da Burkina Faso ba sune kasashe na farko da suka dauki irin wannan mataki da ya shafi Amurkawa ba, bayan gwamnatin Trump ta auna su da irin wannan mataki.

Ranar 25 ga watan  Disemba da ta wuce kasar Nijar makwabciyar wadannan kasashe ta bada sanarwar cewa zata daina bada Visa ga Amurkawa, kamar yadda kafofin yada labaran kasar suka fada, daga bakin masana harkokin difilomasiyyar kasar.

A cikin watan Yuni ne kasar Chadi ta bada sanarwar dakatar da bada visa ga Amurkawa, bayan da gwamnatin Amurkan ta saka kasar a jerin kasashe 12 da haramcinta shafa.

 

Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Post navigation

Previous Post: Tinubu Yace Zayyi Hadaka Da Kasashen Duniya Domin Kawo Karshen Rashin Tsaro.
Next Post: Jamhuriyar Congo Zata Cigaba Da Fitar Da Ma’adanai

Karin Labarai Masu Alaka

Zelensky Na Buƙatar Ganawa Da Trump Domin Cimma Matsaya Kan Batutuwa Masu Sarƙaƙiya Labarai
Ribadu: Najeriya Ce Kasa Daya Tilo Da Ke Tabbatar Da Demokraɗiyya A Sahel Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Shugaba Tinubu Ya Gana Da Wasu Gwamnoni Shida Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Farashin Dalar Amurka Ya Tashi Ranan Juma’a Amurka
Jami’an Tsaro: Babu Abun Tashin Hankali Kan Shawagin Jiragen Amurka Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Gwamnatin Tarayya Ta Cimma Yarjejeniya Da Kungiyar Malaman Jami’oi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Najeriya Ta Dauki Hayan Amurkawa Don Kyautata Alaka Da Trump Game Da Kisan Kiristoci
  • Gwamnatin Tarayya Ta Cimma Yarjejeniya Da Kungiyar Malaman Jami’oi
  • Kabiru Vice: Najeriya Zata Iya Nasara A Kan Moroko AFCON 2025.
  • Motar Yashi Ta Kashe Mutane Shida A Wani Coci Dake Legas
  • An Kaddamar Da Rijistar Zamani Ta Zamowa Mamba A Jam’iyar APC

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • Tinubu Yafara Wasu Dabaru Domin Samun Kuri’u Siyasa
  • NAHCON Tafara Shirye-Shiryen Aikin Hajjin 2026 Najeriya
  • Kirana Ga ‘Yan Siyasar Arewa, Su Jira Sai 2031- Akume Labarai
  • Sojin Israela Sunkai Hari Kan Falatsinawa Tsaro
  • Kasar Afirka Ta Kudu Ta Tsare Wasu Amurkawa Amurka
  • ‘Yan-Bindiga Sun Yi Awon Gaba Da Daliban St. Mary! Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Shugaba Trump Ya Hana Kaiwa Cuba Man Fetur Daga Venezuela Amurka
  • Gwamna Fubara Ya Koma Jam’iyar APC Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.