Man da matatar mai ta Dangote ke fitarwa zuwa kasashen Afirka ya karu sakamakon rikicin Gabas ta Tsakiya, da ya haddasa cikas a samar da makamashi ta hanyoyin da aka saba shiga da fita da su.
Bayanai daga kamfanin dake tantance tankokin dakon mai, Kpler ya nuna cewa dangogin danyen mai da suka hada da man fetur, man diesel, kananzir da man jiragen sama da ake fitarwa daga Nigeria sun karu zuwa a kalla ganga 214,000 a kowacce rana a wannan watan, daga kusan ganga 100,000 da ake fitarwa kowacce rana a watan da ya gabata.
Abinda ake fitarwa zuwa wasu kasashen Afirka ya tashi daga ganga 38,000 zuwa ganga 90,000 kowacce rana.


