Masoya kungiyar kwallan kafa ta kasar Morocco sun nuna farin ciki bisa hukuncin da kotu ta yanke na baiwa kungiyar nasarar cin gasan kwallon kofi na nahiyar Afirka da ci 3-0 kan kasar Senegal. Amma wasu sun ce a bi abun a sannu, yayin da Senegal ke shirin daukaka kara don kalubalantar hukuncin da ya girgiza harkar kwallon kafa a nahiyar afirka.
Hukumar kwallon kafa ta Afirka wato (CAF) ta ayyana kasar Morocco a matsayin wadda ta lashe gasar, bayan da tayi hukuncin cewa ‘yan wasan Senegal sun rasa damar su bayan da suka fice daga fili na tsawon mintuna 14 don nuna adawa da penalty da aka bawa daya bangaren.
Duk da Senegal ta dawo daga baya ta kuma ci kwallo daya a karin lokaci da aka bayar, yayin da Morocco bata ci komai ba, CAF ta sauya sakamakon, inda ta bawa Morocco ci 3, ita kuma Senegal ba ko daya.
Hukumar kwallon kafa ta Senegal tace zata daukaka kara kan wannan hukunci da ba’a taba ganin irin sa ba, kuma baza’a yadda dashi ba. Ita kuma kungiyar kwallon kafa ta Morocco tace daukan tsauraran matakai zai taimakawa kwallon kafa a Afirka.


