Musulmi a kasashe da dama a fadin duniya sun tashi da azumi na watan Ramadhan. Kasar Saudiyya ta sanar da ganin jinjirin watan azumi a jiya Talata, inda hukumomi suka umarci musulmin kasar da su tashi da azumi a yau Laraba.
Haka suma kasashen Kuwait, Yemen, Qatar, Bahrain, Kuwait da Palestine da Nigeria da niger sun sanar da ganin watan. A Amurka ma masallatai sun bada sanarwar fara azumi yau Laraba.
Sauran kasashe kamar Masar, Jordan, Sham, Indonesia da Malaysia basu ga wata ba, saboda haka zasu dauki azumin su ranar Alhamis.


