Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Amurka Tayi Barazanar Zata Rage Tallafin Da Take BayarwaSudan Ta Kudu, Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Farashin Mai Ya Fadi Fiye Da Dala Daya Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Sojojin Najeriya Sun Kashe Fitaccen ’Yan Bindiga Kallamu A Jihar Sakkwato Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya Da Kasar Saudiya Sun Kulla Yarjejeniyar Tsaro Labarai
  • Gwamna Fubara Ya Koma Jam’iyar APC Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Onana Ba Ya Cikin Tawagar Kamaru (AFCON)
Published: December 2, 2025 at 6:45 AM | By: Bala Hassan | Updated: December 2, 2025

Mai tsaron ragar ƙungiyar kwallon kafa ta Kamaru Andre Onana ya sake fuskantar wani mummunan rauni hakan yasa aka cire shi daga tawagar Kamaru da za ta fafata a gasar cin kofin kasashen Afirka da ke tafe.

Dan wasan mai shekaru 29 ya sha wahala a kakar wasa ta 2025-26, bayan ya rasa matsayinsa na mai tsaron raga na 1 a Manchester United kafin aka ba shi damar komawa kungiyar Trabzonspor ta Turkiyya a matsayin aro na tsawon kakar wasa a watan Satumba.

Ba a saka Onana a cikin jerin ‘yan wasa masu tsaron raga hudu ba duk da cewa Kamaru ta zabi ‘yan wasa hudu.

An yi ta jan ido a ranar Litinin lokacin da Kamaru ta fitar da ‘yan wasa 28 da za su fafata a AFCON, wanda za a fara a ranar Lahadi, 21 ga Disamba in da Morocco mai masaukin baki za ta fafata da Comoros.

Duk da zabar masu tsaron gida hudu, Onana bai shiga cikin jerin ‘yan wasan Indomitable Lions ba.

‘Yan wasa biyu da aka sanya a cikin tawagar sune dan wasan gaba na United Bryan Mbeumo da dan wasan tsakiya na Brighton & Hove Albion Carlos Baleba, wanda aka alakanta da komawa Old Trafford a lokacin bazara.

Tsohon ɗan wasan gefe na Tottenham Hotspur Georges-Kevin Nkoudou – wanda yanzu yake bugawa ƙungiyar Diriyah Club ta Saudiyya wasa – shi ma ƙasarsa ta zaɓe shi.

A hukumance: Tawagar ‘yan wasa 28 na Kamaru wadanda ba su hada da Onana ba

Tawagar Kamaru ta 2025 AFCON:

Masu tsaron gida: Devis Epassy, ​​Simon Omossola, Simon Ngapandouetnbu, Edouard Sombang

Masu tsaron baya: Samuel Junior Kotto, Gerzino Nyamsi, Jean-Charles Castelletto, Nouhou Tolo, Flavien Enzo Boyomo, Nagida Mahamadou, Junior Tchamadeu, Christopher Wooh, Darlin Yongwa

‘Yan wasan tsakiya: Martin Ndzie, Carlos Baleba, Arthur Avom, Eric Junior Dina Ebimbe, Fidel Brice Ambina, Danny Namaso, Christian Bassogog, Georges-Kevin Nkoudou, Jean Junior Onana, Olivier Kemen

Masu wasan gaba: Bryan Mbeumo, Christian Kofane, Frank Magri, Karl Etta Eyong, Patrick Soko.

Hukumar Kwallon Kafa ta Kamaru ta kori kocin da ya lashe gasar AFCON sau biyar a rana ɗaya.

 

Hukumar Kwallon Kafa ta Kamaru – karkashin jagorancin tsohon dan wasan Barcelona, Chelsea da Inter Milan Samuel Eto’o – ta salami mai horaswa Marc Brys a ranar da aka sanar da sunayen ‘yan wasan da zasu  fafata mata a gasar cin kofin kasashen Afirka AFCOB

Inda suka nada David Pagou a matsayin wanda zai maye gurbin Brys, kasar Kamaru za su fafata da Gabon a wasan farko cikin makonni uku kacal (24 ga Disamba). Kamaru kuma za ta fafata da Ivory Coast (28 ga Disamba) da Mozambique (31 ga Disamba) a matakin rukuni.

Wasanni

Post navigation

Previous Post: Wasan Hamayya (Istanbul Derby) Fenerbahçe Da Galatasaray 1-1
Next Post: Magoya Bayan Nice Sun Kai Hari Wa ‘Yan Wasansu

Karin Labarai Masu Alaka

Wasu Zakaru Da Suka Samu Karramawar Hukumar CAF Ta Afrika Wasanni
Madrid, Arsenal Da Chelsea Sun Fara Zaurancen Dan-Wasa Kenan Yildiz Wasanni
Manya-Manyan Wasannin Wannan Makon Wasanni
FIFA, Ta Raba Jaddawalin Rukuni Na Gasar Kofin Duniya 2026. Wasanni
Kocin Zambia Na Mata Ba Lafiya Labarai
Bana Ba Harka Ga ‘Yan-Wasan Kwallon Kafar Najeriya Wasanni

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Shirin Manuniya Yau Juma’a 12.12.2026
  • Ministan Tsaro Ya Umarci Janye Sojoji Daga Shingayen Bincike A Tituna
  • Atiku Ya Zargi Gwamnati Da Kama ‘Yan Adawa
  • Rashin Tsaro: Gwamnati Ta Bada Umarnin Daukar Ma’aikata Sama Da 94,000
  • Najeriya Ta Gabatar Da Tayin Karbar Bakoncin Wasannin Afirka Na 2031

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Rediyo
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • Mun Kwato Kimanin Naira Biliyan 40 Na Badakala A Tsawon Shekara Daya Labarai
  • Shirin: Lafiya Jari Ce 11.21.25 Kiwon Lafiya
  • Ga Fili Ga Doki Najeriya
  • Shirin Dare 2030 UTC Yau Asabar 11.15.2025 Rediyo
  • Gwamnatin Tarayya Tana Neman Kudi Domin Aiwatar Da Kasafin Kudin 2026 Najeriya
  • Gwamnatin Bauchi Ta Amince Domin Inganta Kasuwancin Nama A Jihar Labarai
  • An Kafa Majalisar Kotun Sulhu Ta Kano Labarai
  • Shirin Safe 0500 UTC Yau Alhamis 11.20.2025 Rediyo
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.