Daukan tsauraran matakai da hukumomin kasar Iran sukayi kan masu zanga-zanga ya shawo kan abun, hargitsi ya dan lafa a yanzu, a cewar mazauna wajen ranar Jumu’a, yayin da kafar talabijin ta kasar ta ruwaito cewa an sake yin Kamen mutane.
Shugaban Amurka Donald Trump ya sha barazanar kai wa masu zanga-zanga dauki idan aka ci gaba da kashe su.
Trump, wanda barazanar tasa ta hada da yin alwashin daukan mataki me karfi idan ta zartar da hukuncin kisa kan masu zanga-zanga, ya ce hukumomi a Tehran sun fasa kudurin su na rataye mutane da dama.
Trump ya wallafa a shafin sa na sada zumunta cewa yana farin cikin cewa shugabannin Iran sun fasa kaddamar da hukunci rataya ga mutane da yawa, wajen su 800 da ya kamata a yi jiya, Na gode, in ji shi.
Iran bata sanar cewa zata yi wannan hukunci ba, kuma bata ce ta soke ba.
Rikici ya barke a Iran ne ranar 28 ga Watan Disamba saboda matsin tattalin arziki, abunda ya munana zuwa zanga-zangar adawa ga gwamnati a fadin kasar, da ke kira da kawo karshen mulkin shugabbannin addini.


