Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Najeriya Ta Dauki Hayan Amurkawa Don Kyautata Alaka Da Trump Game Da Kisan Kiristoci Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnatin Tarayya Ta Cimma Yarjejeniya Da Kungiyar Malaman Jami’oi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Amurka Ta Baiwa Najeriya Wasu Muhimman Kayan Yaki Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Trump Yayi Kira Ga ‘Yan Ƙasar Iran Su Ci Gaba Da Zanga Zanga Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Syria: Mutane Sun Yi Zanga Zanga Domin Nuna Rashin Amincewa Da Korar Kurdawa A Birnin Aleppo Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Rundunar Hadinkan Saudiya Tayi Ikirarin Mayar Da Martani Ga ‘Yan Aware
Published: December 27, 2025 at 9:24 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Rundunar hadin kai da Saudiyya take yiwa jagoranci a Yemen tace zata maida martani kan duk wani yunkurin da ‘yan aware dake kudancin lardin Hadaramount suka yi, wadda ka iya illa ga kokarin tsagaita wuta kamar yadda Kamfanin dilancin labarai na Saudiyya ya bayyana a yau Asabar.

Sanarwar da kakakin rundunar hadin guiwa Janar Turki al-Maliki ya bayar, ya biyo bayan bukatar da shugaban majalisar gudanarwa a Yemen,Rashad al-Alimi yayi na daukar matakan gaggawa domin kare farar hula a lardin Hadaramount bayanda mayaka wadanda suke da alaka da kungiyar ‘yan tawaye da ake yiwa lakabi da STC suka keta yarjejenyar da take aiki na tsagaita wuta

Kungiyar ‘yan tawayen STC watau Southern Transitional Council da turanci, wacce hadaddiyar daular larabawa take marawa baya, ta hambare gwamnatin yankin da Saudiyya da kuma kasashen duniya suka amince data ita a farkon watan nan daga helkwatarta dake Aden, kuma ta ayyana iko a duk fadin kudancin kasar.

A ranar Jumma’a dai kunigyar ta STC tayi watsi da kiran da Saudiyya tayi mata cewa ta janye daga sassan data kama a farkon watan nan, tana mai cewa zata ci gaba da aikin mamaye lardunan dake kudancin Yemen da ake kira Hadaramount da Mahra.

Daga bisani anji ministan tsaron Saudiyya Yerima Khalid Bin Salman, ta wani sako da ya wallafa a shafinsa na X, yana kira ga Kungiyar ta STC ta saurari kokarin sulhu da ake yi, kuma ta amince da a gudanar da shawarwari da nufin shawo kan rikici a yankin.

Labarai

Post navigation

Previous Post: Gwamnatin Najeriya Tace Ta Farmaki Mayakan ISIS A Jihar Sokoto
Next Post: Kasashen Thailand Da Cambodia Sun Amince Da Tsagaita Wuta

Karin Labarai Masu Alaka

Mayakan M23 Sun Tsagaita Wuta A Gabashin Kwango Labarai
‘Yan Tawayen M23 Masu Samun Goyon Bayan Rwanda Basu Jamye A Ulvira Ba Labarai
Babangida: Hakika Abiola Ya Lashe Zaben Watan Yuni 1993 Labarai
Kocin Zambia Na Mata Ba Lafiya Labarai
Za’a Fuskanci Bala’in Yunwa A Najeriya Labarai
Malami: Gwamnatin APC Ta Gaza – “Yan-Kasa Kuwa Na Da Katin Zabe” Labarai

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Najeriya Ta Dauki Hayan Amurkawa Don Kyautata Alaka Da Trump Game Da Kisan Kiristoci
  • Gwamnatin Tarayya Ta Cimma Yarjejeniya Da Kungiyar Malaman Jami’oi
  • Kabiru Vice: Najeriya Zata Iya Nasara A Kan Moroko AFCON 2025.
  • Motar Yashi Ta Kashe Mutane Shida A Wani Coci Dake Legas
  • An Kaddamar Da Rijistar Zamani Ta Zamowa Mamba A Jam’iyar APC

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • Manchester United: Za Ta Nada Michael Carrick A Matsayin Kocin Riƙon ƙwarya Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Amurka Na Shirin Kauracewa Taron Kungiyar Kasashen G20 Afrika
  • Hukumar Tsaro Ta DSS Ta Aika Sammaci Dr. Yusuf Baba-Ahmed Labarai
  • Tinubu: Abba Magajin Aminu Kano Ne A Fagen Siyasa Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Nuhu Ribadu Ya Mika Dalibai 100 da Aka Ceto Ga Gwamnatin Jihar Neja Labarai
  • ECOWAS Ta Saka Dokar Ta Baci A Afrika Ta Yamma Afrika
  • Shugaba Trump Yace Amurka Ce Zata Rika Gudanar Da Harkokin Kasar Venezuela Amurka
  • Motar Yashi Ta Kashe Mutane Shida A Wani Coci Dake Legas Najeriya
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.