Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Zelensky: Gabas Ta Tsakiya Na Iya Nuna Makomarmu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Mojtaba Khamenei Ya Zama Sabon Jagoran Jamhuriyar Musulunci ta Iran Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnatin Najeriya Taja Hankalin ‘Yan Najeriya Mazauna Iran Da Kasashen Larabawa Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnan Gombe Yace An Sace Yara 48 A Jihar Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • ‘Yan Bindiga Suna Cigaba Da Kashe Mutane A Garin Gwana Dake Jihar Bauchi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Rundunar Hadinkan Saudiya Tayi Ikirarin Mayar Da Martani Ga ‘Yan Aware
Published: December 27, 2025 at 9:24 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Rundunar hadin kai da Saudiyya take yiwa jagoranci a Yemen tace zata maida martani kan duk wani yunkurin da ‘yan aware dake kudancin lardin Hadaramount suka yi, wadda ka iya illa ga kokarin tsagaita wuta kamar yadda Kamfanin dilancin labarai na Saudiyya ya bayyana a yau Asabar.

Sanarwar da kakakin rundunar hadin guiwa Janar Turki al-Maliki ya bayar, ya biyo bayan bukatar da shugaban majalisar gudanarwa a Yemen,Rashad al-Alimi yayi na daukar matakan gaggawa domin kare farar hula a lardin Hadaramount bayanda mayaka wadanda suke da alaka da kungiyar ‘yan tawaye da ake yiwa lakabi da STC suka keta yarjejenyar da take aiki na tsagaita wuta

Kungiyar ‘yan tawayen STC watau Southern Transitional Council da turanci, wacce hadaddiyar daular larabawa take marawa baya, ta hambare gwamnatin yankin da Saudiyya da kuma kasashen duniya suka amince data ita a farkon watan nan daga helkwatarta dake Aden, kuma ta ayyana iko a duk fadin kudancin kasar.

A ranar Jumma’a dai kunigyar ta STC tayi watsi da kiran da Saudiyya tayi mata cewa ta janye daga sassan data kama a farkon watan nan, tana mai cewa zata ci gaba da aikin mamaye lardunan dake kudancin Yemen da ake kira Hadaramount da Mahra.

Daga bisani anji ministan tsaron Saudiyya Yerima Khalid Bin Salman, ta wani sako da ya wallafa a shafinsa na X, yana kira ga Kungiyar ta STC ta saurari kokarin sulhu da ake yi, kuma ta amince da a gudanar da shawarwari da nufin shawo kan rikici a yankin.

Labarai

Post navigation

Previous Post: Gwamnatin Najeriya Tace Ta Farmaki Mayakan ISIS A Jihar Sokoto
Next Post: Kasashen Thailand Da Cambodia Sun Amince Da Tsagaita Wuta

Karin Labarai Masu Alaka

An Gudanar Da Jana’izar ’Yan Jaridan Da Suka Rasu A Jihar Gombe Labarai
Kungiyar Kiristoci Ta Wanke Gwamnan Bauchi Daga Zargin Ta’addanci Labarai
Aikin Layin Dogon Kasar Uganda Zai Hade Kasar Da Tanzania Da Kwango Kimiya
Wakilan Majalisar Dokokin Phillipines Suna Yunkurin Tsige Shugaban Kasar Afrika
Gobara Ta Lalata Shaguna Da Gidajen Abinci A Gombe Labarai
Hukumomin Tsaron Kenya Sunce ‘Yan Kasar Suna Fafata Yaki Da Dakarun Rasha A Ukraine Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • ‘Yan Uwa Musulmi A Jihar Gombe Sunyi Allah Wadai Da Kisan Ayatollah Khomeini
  • An Samu Kaburbura Biyu Dauke Da Gawarwaki 173 A Kasar Kwango
  • Yan Bindiga Suna Cigaba Da Kashe Mutane A Garin Gwana Dake Jihar Bauchi
  • Karancin Iskar Gas Kalubale Ne Ga Wutar Lantarki
  • Zelensky: Gabas Ta Tsakiya Na Iya Nuna Makomarmu

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • Oliseh, Ya Ba Eric Chelle, Shawara Da Ya Zamo Mai Tsauri AFCON 2025. Wasanni
  • Shugaban Kare Hakkin Dan Adam Na Majalisar Dinkin Duniya Yace RSF Sun Aikata Zalunci Afrika
  • Kasashen Daular Larabawa Tare Da Saudiya Da Jordan Sunyi Allah Wadai Da kasar Israel Afrika
  • Dubban ‘Yan Gudun Hijira Sun Halaka Amurka
  • ‘Yansandan Uganda Sun Tsare ‘Yar Fafutukar Kare Hakkin Bil’adama Sarah Bireete Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Kotun Uganda Tayi Watsi Da Karar Hukumomin Kasar Afrika
  • Usman Maiyama Ne Gwarzon Kamun Kifin Argungu Bana Labarai
  • Tinubu: Ku Guji Yi Wadaka Da Kudin Kananan Hukumomi Najeriya
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.