Sabon shugaban addinin Islama na ran, Mojtaba Khameni, yaji rauni, kuma watakil ya nakasa, inji sakataren tsaron Amurka Pete Hegseth a jiya jumma’a, har yana tababar yadda za’a yi Mojtaban ya jagoranci kasar, bayan mako biyu na hare haren da Amurka da Isra’ila suke kaiwa kan kasar.
A ranar Alhamis ne aka ji kalaman farko daga sabon shugaban addini na Iran da aka karanta a talabijin. A cikin sanarwar yayi alawashin ci gaba da rufe mashigin ruwan Hormuz, ya kuma yi kira ga kasashe makwabta su rufe dukkan sansanonin Amurka dake kasashen su, ko kuma su fuskanci kasadar Iran ta auna su a hare haren da take kaiwa.
“Iran tana da kamarori masu yawa, da na’uororin daukar magana, me yasa sai a rubuce zai yi magana, Ina ji kun san dalili. Mahaifinsa ya mutu, a tsorace yake, ko ya ji rauni, ko kuma yana kan gudu, domin ba shugaba ne halattacce ba.”
Zuwa yanzu dai babu wani hotonsa da aka gani tun harin farko da Isra’ila ta kai ya kashe iyayensa harda matarsa.
A wani mataki kuma, Amurka tana tayin bada tukuici dala milyan 10 kan duk wadda zai bata labarin ko bayanai dangane manyan jami’an soji dana leken asirin Iran, ciki harda sabon shugaban addinin kasar Ayatollah Mojtaba Khameni.


