Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Najeriya Ta Dauki Hayan Amurkawa Don Kyautata Alaka Da Trump Game Da Kisan Kiristoci Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnatin Tarayya Ta Cimma Yarjejeniya Da Kungiyar Malaman Jami’oi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Amurka Ta Baiwa Najeriya Wasu Muhimman Kayan Yaki Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Trump Yayi Kira Ga ‘Yan Ƙasar Iran Su Ci Gaba Da Zanga Zanga Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Syria: Mutane Sun Yi Zanga Zanga Domin Nuna Rashin Amincewa Da Korar Kurdawa A Birnin Aleppo Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Sakataren Gwamnatin Amurka Ya Bayyana Bawa Kungiyoyin Agaji Damar Kai Taimako Sudan
Published: December 20, 2025 at 7:41 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Sakataren gwamnatin Amurka, Marco Rubio, ranar Jumu’a, yace burin fadar Washington kan Sudan a yanzu shi ne mayar da makaman yaki, har zuwa cikin sabuwar shekara, don barin kungiyoyin agaji su kai taimako.

Yayin da yake jawabi ga ‘yan jarida a wani taro da Manema labarai, Rubio ya ce kasashe suna bawa bangarori makamai, ciki har da aikewa da Makamai musamman ga dakarun sa kai, inda ya kara da cewa fadar Washington na tattaunawa da bangarorin da abun ya shafa.

Ya ce sun tattauna a kan abubuwan da suka dace da duka bangarorin, saboda ba wani bangare da zai iya wani tasiri ba tare da goyon bayan daya bangaren ba, shi yasa muke tattaunawa da duka bangarorin da ke da ruwa da tsaki a wannan abu.

Hukumomin Amurka sun ce sojojin kasar sun kai hare hare da jiragen sama kan sansanin kungiyar ‘yan ta’adda na ISIS da dama a Syria ranar Jumu’a, a wani martani da aka yi kan Jami’an Amurka.

Shugaba Donald Trump ya dau alwashin mai da martani bayan da wani da ake zargin dan ISIS ne ya kaiwa jami’an Amurka hari a karshen makon da ya gabata a Syria.

Sakataren tsaron Amurka Pete Hegseth, ya tabbatar da hare-haren sun fada ne kan mayakan ISIS, kayayyakin su, da makaman su, Kuma ya ce taken harin shi ne OPERATION HAWKEYE STRIKE.

Ya kara da cewa, wannan ba mafarin yaki ba ne, ramuwar gayya ce, yau mun farauto, kuma mun kashe makiyan mu.

Amurka

Post navigation

Previous Post: An Kashe Falatsinawa Biyar A Wani Hari Da Isra’ila Takai Wata Makaranta A Gaza
Next Post: Shugaban Najeriya Bola Tinubu Zai Ziyarci Jihohin Borno,Bauchi Da Legas

Karin Labarai Masu Alaka

‘Yan Tawayen Kungiyar M23 Sun Tsagaita Sakamakon Rokon Da Amurka Tayi Amurka
Ana Zargin Cewa ‘Yan Bindiga Biyun Nan Mambobin Kungiyar ISIS Ne Amurka
Kasar Amurka Ta Sayi Kamfanin Sada Zumunci Na Tik-Tok Amurka
Kasar Amurka Tabada Tabbacin Bawa Ukraine Tsaron Shekarun 15 Amurka
Shugaban Kasar Amurka Yakara Hana Wasu Kasashe Shiga Amurka Ciki Harda Nijar Amurka
Ministan Kudin Botswana Yace Akwai Hasashen Cewa Tattalin Arzikin Kasar Zai Ragu Amurka

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Najeriya Ta Dauki Hayan Amurkawa Don Kyautata Alaka Da Trump Game Da Kisan Kiristoci
  • Gwamnatin Tarayya Ta Cimma Yarjejeniya Da Kungiyar Malaman Jami’oi
  • Kabiru Vice: Najeriya Zata Iya Nasara A Kan Moroko AFCON 2025.
  • Motar Yashi Ta Kashe Mutane Shida A Wani Coci Dake Legas
  • An Kaddamar Da Rijistar Zamani Ta Zamowa Mamba A Jam’iyar APC

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • Gwamnan Jihar Gombe Ya Umurci A Rufe Makarantu Labarai
  • Ministan Tsaron Najeriya Badaru Yayi Murabus Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Sojoji Sun Yi Juyin Mulki A Guinea Bissau Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • CAF Ta Fara Binciken Rikicin Bayan Wasa Tsakanin Algeria Da Najeriya Wasanni
  • Amurka Zata Bawa Ukraine Tsaro Na Musamman Amurka
  • Ana Jimamin Mutuwar Giwa Mai Shekaru Kusan 60 A Kasar Kenya Sauran Duniya
  • Jihar Gombe Tayi Fice A Bangaren Inganta Lafiya Matakin Farko Najeriya
  • Ministan Kudin Botswana Yace Akwai Hasashen Cewa Tattalin Arzikin Kasar Zai Ragu Amurka
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.