Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Zelensky: Gabas Ta Tsakiya Na Iya Nuna Makomarmu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Mojtaba Khamenei Ya Zama Sabon Jagoran Jamhuriyar Musulunci ta Iran Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnatin Najeriya Taja Hankalin ‘Yan Najeriya Mazauna Iran Da Kasashen Larabawa Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnan Gombe Yace An Sace Yara 48 A Jihar Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • ‘Yan Bindiga Suna Cigaba Da Kashe Mutane A Garin Gwana Dake Jihar Bauchi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Sakataren Gwamnatin Amurka Ya Bayyana Bawa Kungiyoyin Agaji Damar Kai Taimako Sudan
Published: December 20, 2025 at 7:41 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Sakataren gwamnatin Amurka, Marco Rubio, ranar Jumu’a, yace burin fadar Washington kan Sudan a yanzu shi ne mayar da makaman yaki, har zuwa cikin sabuwar shekara, don barin kungiyoyin agaji su kai taimako.

Yayin da yake jawabi ga ‘yan jarida a wani taro da Manema labarai, Rubio ya ce kasashe suna bawa bangarori makamai, ciki har da aikewa da Makamai musamman ga dakarun sa kai, inda ya kara da cewa fadar Washington na tattaunawa da bangarorin da abun ya shafa.

Ya ce sun tattauna a kan abubuwan da suka dace da duka bangarorin, saboda ba wani bangare da zai iya wani tasiri ba tare da goyon bayan daya bangaren ba, shi yasa muke tattaunawa da duka bangarorin da ke da ruwa da tsaki a wannan abu.

Hukumomin Amurka sun ce sojojin kasar sun kai hare hare da jiragen sama kan sansanin kungiyar ‘yan ta’adda na ISIS da dama a Syria ranar Jumu’a, a wani martani da aka yi kan Jami’an Amurka.

Shugaba Donald Trump ya dau alwashin mai da martani bayan da wani da ake zargin dan ISIS ne ya kaiwa jami’an Amurka hari a karshen makon da ya gabata a Syria.

Sakataren tsaron Amurka Pete Hegseth, ya tabbatar da hare-haren sun fada ne kan mayakan ISIS, kayayyakin su, da makaman su, Kuma ya ce taken harin shi ne OPERATION HAWKEYE STRIKE.

Ya kara da cewa, wannan ba mafarin yaki ba ne, ramuwar gayya ce, yau mun farauto, kuma mun kashe makiyan mu.

Amurka

Post navigation

Previous Post: An Kashe Falatsinawa Biyar A Wani Hari Da Isra’ila Takai Wata Makaranta A Gaza
Next Post: Shugaban Najeriya Bola Tinubu Zai Ziyarci Jihohin Borno,Bauchi Da Legas

Karin Labarai Masu Alaka

Trump Zai Sasanta Tsakanin Masar Da Habasha Amurka
Sabon Magajin Garin New York Zai Soke Wasu Dokoki Amurka
Shugaban Kasar Brazil: Yakamata Amurka Ta Gurfanar Da Shugaban Venezuela A Kotu Afrika
‘Yan Sanda Sunce Mutum Daya Ne Yakai Hare-Haren Jami’ar Brown Da Kuma Na MIT Boston Amurka
Shugaba Trump Yayi Barazanar Tura Sojoji Ga Masu Zanga Zanga Amurka
Tsohon Lauyan Amurka Jack Smith Ya Fadi Maganganu Game Da Donald Trump Amurka

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • ‘Yan Uwa Musulmi A Jihar Gombe Sunyi Allah Wadai Da Kisan Ayatollah Khomeini
  • An Samu Kaburbura Biyu Dauke Da Gawarwaki 173 A Kasar Kwango
  • Yan Bindiga Suna Cigaba Da Kashe Mutane A Garin Gwana Dake Jihar Bauchi
  • Karancin Iskar Gas Kalubale Ne Ga Wutar Lantarki
  • Zelensky: Gabas Ta Tsakiya Na Iya Nuna Makomarmu

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • Kwankwaso Yayi Kakkausar Lafazi Bayan Ficewar Abba Kabir Yusuf Daga NNPP Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • An Tsinci Gawar Yarinya A Gombe Najeriya
  • ‘Yan Sanda Sun Kama Masu Garkuwar da Mutane a Jihar Gombe Tsaro
  • Kamfanin Bitcoin A Korea Ta Kudu Yayi Kuskuren Turawa Masu Mu’amala Da Kamfanin Kudade Afrika
  • Akalla Mutane 8 Sun Mutu Biyo Bayan Bindiga Da Wata Tanka Tayi Afrika
  • Afirka Ta Kudu Ta Bayyana Yadda Aka Yaudari ‘Yan Kasar Ake Tilasta Musu Ayyukan Bauta Afrika
  • Kasar Colombia Tare Da Amurka Zasu Fitar Da Man Venezuela Labarai
  • CAN: Da Alamu Daliban St. Mery Na Cikin Koshin Lafiya Najeriya
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.