Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Najeriya Ta Mika Koke Ga FIFA Tana Zargin DR Congo Ta Sanya ‘Yan Wasan Da Basu Cancantaba Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • ‘Yan Tawayen M23 Masu Samun Goyon Bayan Rwanda Basu Jamye A Ulvira Ba Labarai
  • Afirka Ta Kudu Ta Kama ‘Yan ƙasar Kenya Su Bakwai Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • ‘Yan Bindiga Sun Kama Akalla Mutane 13 A Wani Coci A Jihar Kogi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Ahmed Musa, Yayi Ritaya A ƙwallon ƙasa Da ƙasa Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Sanyin Hunturu Yayi Ajalin ‘Yan Cirani A Morocco
Published: December 15, 2025 at 9:14 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Sanyi mai tsanani ya kase wasu bakin haure ‘yan Afirka a kusa da bakin iyakar Morocco da Aljeriya.

Kungiyoyin kare hakkin bil Adama a kasar dake Afirka ta Arewa sun bayyana wannan a matsayin babban abin damuwa kuma abinda ya keta ‘yancin zirga-zirgar murtane.

Wata gamayyar kungiyoyin kare hakkin bil Adama a kasar Morocco, ta ce an gano gawarwakin maza 7 da mata biyu a yankin Ras Afour mai tsaunuka, inda sanyin hunturu yake yayi tsanani sosai.

Kungiyar ta ce wadannan bakin haure ‘yan gudun hijira sun mutu a sanadiyyar sanyi mai tsanani wanda jikinsu dake gajiye ba zai iya dauka ba.

An ce daya daga cikin ‘yan gudun hijirar dan kasar Guinea ne.

A duk shekara, dubban ‘yan Afirka dake kwadayin zuwa kasashen turai su na bi ta cikin hamadar Sahara zuwa kasashen Afirka ta yamma daga inda suke fatan tsallakawa zuwa turai, amma irin wannan balaguro yana da tsananin hadari, kuma daruruwa suna mutuwa ba tare da sun kai inda suke son zuwa ba.

Afrika

Post navigation

Previous Post: Kasar Ukraine Tayi Watsi Da Shiga Kungiyar NATO
Next Post: Gwamnatin Tarayya Na Kokarin Hana Demokraɗiyya A Najeriya

Karin Labarai Masu Alaka

Shugaban Guinea-Bissau Umaro Na Fuskantar Matsin Lamba Afrika
Kasar Belarus Zata Taffawa Jamhuriyar Nijar Afrika
Kungiyar ECOWAS Ta Koka Game Da Yawan Juyin Mulki A Kasashen Afirka Afrika
Burkina Faso: Mun Kama Sojojin Najeriya da Jirgin Yaki Bisa Shigowa Ba Bisa Ka’ida Ba Afrika
ECOWAS Ta Saka Dokar Ta Baci A Afrika Ta Yamma Afrika
Nijar: Zamu Tsananta Bincike A Bakin Iyakokin Mu Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Najeriya Ta Mika Koke Ga FIFA Tana Zargin DR Congo Ta Sanya ‘Yan Wasan Da Basu Cancantaba
  • Tsohon Dankarar Gwamnan PDP A Gombe Ya koma ADC
  • FIFA Ta Yi Wa Malaysia Kaca-kaca
  • Najeriya Ta Kai Wasan Kusa Da Na Karshe A Wasan Dambe Na Matasan Afirka
  • Burkina Faso Ta Sako Jami’an Rundunar Sojin Saman Najeriya 11 Da Aka Tsare

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • Akwai Bukatar Bin Dokokin Tuki A Kan Hanyoyi Labarai
  • ECOWAS Zata Kafa Rundunar Yaki Da Rashin Tsaro Afrika
  • Shirin Dare 2030 UTC Yau Laraba 11.19.2025 Rediyo
  • Tabbas Za’a Gudanar Da Gasar Firimiya Lig Ta Najeriya Wasanni
  • Wasan Hamayya (Istanbul Derby) Fenerbahçe Da Galatasaray 1-1 Labarai
  • Nasarawa Ce Zakara A Wasan Kwallon Kafa Ta Kurame 2025 Wasanni
  • Kauran Bauchi: Muna Nan A PDP Daram! Siyasa
  • An Kai Hari Da Jirgi Mara Matuki A Kusa Da Matatar Mai Din Kasar Sundan Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.