Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Shugaban Amurka Zai Sake Aika Jirgin Yaki Gabas Ta Tsakiya Amurka
  • Dalibin Jami’a Ya Rasa Ransa A Birnin Dakar Yayin Zanga Zanga Afrika
  • Maikaba Ya Yi Murabus A Matsayinsa Kocin Wikki Tourist FC Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • NEDC : Zata Samar Da Cikekken Kulawa Wa ‘Yan Jaridar Da Sukayi Hatsari A Bauchi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnatin Trump Zata Kafa Kasuwar Ma’adanai Amurka

Sanyin Hunturu Yayi Ajalin ‘Yan Cirani A Morocco
Published: December 15, 2025 at 9:14 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Sanyi mai tsanani ya kase wasu bakin haure ‘yan Afirka a kusa da bakin iyakar Morocco da Aljeriya.

Kungiyoyin kare hakkin bil Adama a kasar dake Afirka ta Arewa sun bayyana wannan a matsayin babban abin damuwa kuma abinda ya keta ‘yancin zirga-zirgar murtane.

Wata gamayyar kungiyoyin kare hakkin bil Adama a kasar Morocco, ta ce an gano gawarwakin maza 7 da mata biyu a yankin Ras Afour mai tsaunuka, inda sanyin hunturu yake yayi tsanani sosai.

Kungiyar ta ce wadannan bakin haure ‘yan gudun hijira sun mutu a sanadiyyar sanyi mai tsanani wanda jikinsu dake gajiye ba zai iya dauka ba.

An ce daya daga cikin ‘yan gudun hijirar dan kasar Guinea ne.

A duk shekara, dubban ‘yan Afirka dake kwadayin zuwa kasashen turai su na bi ta cikin hamadar Sahara zuwa kasashen Afirka ta yamma daga inda suke fatan tsallakawa zuwa turai, amma irin wannan balaguro yana da tsananin hadari, kuma daruruwa suna mutuwa ba tare da sun kai inda suke son zuwa ba.

Afrika

Post navigation

Previous Post: Kasar Ukraine Tayi Watsi Da Shiga Kungiyar NATO
Next Post: Gwamnatin Tarayya Na Kokarin Hana Demokraɗiyya A Najeriya

Karin Labarai Masu Alaka

Kasar Habasha Ta Cimma Matsaya Da Masu Binta Bashi Afrika
An Gano Kwale-Kwalen Fir’auna A Birnin Masar Afrika
Afirka Ta Kudu Ta Bukaci Jakadan Israela Ya Fice Daga Kasar Afrika
Amurka Ta Kama Tsohon Ministan Kudin Kasar Ghana Afrika
Kasar Togo Ta Kori Paul Henri Damiba Zuwa Kasar Sa Ta Haihuwa Afrika
Muna Kira Ga Kasashen Duniya Su Sa Baki Don A Saki Mohamed Bazoum Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Shugaban Amurka Zai Sake Aika Jirgin Yaki Gabas Ta Tsakiya
  • Dalibin Jami’a Ya Rasa Ransa A Birnin Dakar Yayin Zanga Zanga
  • Kasar Zimbabwe Ta Samar Da Dokar Tsawaita Mulkin Mnangagwa Zuwa 2030
  • ‘Yan Bindiga Sun Karya Alkawarin Dakatar Da Kai Hare Hare A Najeriya
  • Amurka Zata Bawa Sojojin Najeriya Horo

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • Shugaba Trump Yayi Barazanar Tura Sojoji Ga Masu Zanga Zanga Amurka
  • Atiku Ya Zargi Gwamnati Da Kama ‘Yan Adawa Labarai
  • Ana Cigaba Da Tattaunawa Tsakanin Trump Da Zelensky Domin Tsagaita Wuta A Ukraine Labarai
  • An Kashe Mutane 7 A Unguwar Dorayi Dake Kano Najeriya
  • Gwamnatin Kano Ta Samar Da Wasu Dabarun Inganta Tsaro Tsaro
  • Ukraine Ta Mika Wa Amurka Daftarin Yarjejeniya Da Rasha Sauran Duniya
  • Zamu Hana Wasu ‘Yan-Najeriya Visa Shiga Amurka Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Zamu Hada Kai Mu Yaki Cutar Shan’inna (Polio) Labarai
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.