Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Maikaba Ya Yi Murabus A Matsayinsa Kocin Wikki Tourist FC Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • NEDC : Zata Samar Da Cikekken Kulawa Wa ‘Yan Jaridar Da Sukayi Hatsari A Bauchi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnatin Trump Zata Kafa Kasuwar Ma’adanai Amurka
  • An Yanke Mishi Hukuncin Kisa Saboda Neman Kudin Aure Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Babban Malamin Musulunci Sheikh Usman Kusfa Zaria Ya Rasu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Shugaba Tinubu: Naji Dadin Sako Daliban Neja Da Aka Sace
Published: December 8, 2025 at 8:03 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu ya jinjinawa hukumomin tsaro bisa kokarinsu na kubutar da dalibai 100 na makarantar Papiri Catholic School da ke Jihar Neja.

Yayin da ya bayyana farin cikinsa kan dawowar daliban cikin lafiya, Shugaba Tinubu ya kuma umarci hukumomin tsaro da su tabbatar da gaggawar kubutar da sauran dalibai 115 da malamansu da ke hannun masu garkuwa.

Shugaban Kasar ya tabbatar wa iyayen daliban cewa gwamnatin tarayya tare da gwamnatin Jihar Neja na aiki tare domin ganin an dawo da dukkan wadanda aka sace cikin koshin lafiya.

“Ina da cikakken bayani kan dawowar dalibai 100 na makarantar Catholic da ke Jihar Neja.

Ina murnar wannan cigaba tare da Gwamna Umar Bago, kuma ina yabawa hukumomin tsaro bisa jajircewarsu tun bayan mummunan lamarin da ya faru ranar 21 ga Nuwamba.

“Umarni na ga hukumomin tsaro a bayyane yake, dole ne a ceto dukkan daliban da sauran ’yan Najeriya da aka sace, a dawo da su gida lafiya sannan dole mu tabbatar da an ciro kowa ba tare da barin kowa a baya ba.

Gwamnatin tarayya za ta ci gaba da aiki tare da jihar Neja da sauran jihohi domin kara tsaro a makarantun mu da samar da mafi ingancin muhalli na ilmantarwa ga yaranmu.

“Daga yanzu, hukumomin tsaro tare da haɗin gwiwar gwamnoni dole su dakile sake faruwar irin wadannan sace sacen, ya kuma zama wajibi yaranmu su daina zama a wajajen da ’yan ta’adda za su rika kai hari don karya karatunsu da jefa kan su da iyalansu cikin bakin ciki,” in ji Shugaba Tinubu.

Labarai

Post navigation

Previous Post: Dangantaka Tayi Tsamari Tsakanin Salah Da Slot.
Next Post: An Samar Da Dala Kusan Biliyan Biyu Don Yakar Polio

Karin Labarai Masu Alaka

Kasar Iceland Ta Kauracewa Bikin Gasar Wakokin Shekara Mai Zuwa Labarai
Hukumar Tsaro Ta DSS Ta Aika Sammaci Dr. Yusuf Baba-Ahmed Labarai
Zelensky Na Ukraine Zai Gana Da Takwaransa Na Faransa A Yau Labarai
Mutum Mafi Tsufa A Saudiyya Ya Rasu Yana Da Shekaru 142 Labarai
Kotun Kasar Rasha Ta Daure Dan Kasar Belarus Shekarar 22 A Kurkuku Labarai
Maharan Bindiga Sun Kashe Mutane 12 Masu Hakar Ma’adanai A Jihar Filato Labarai

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Indonesia Zata Kafafa Rundunar Kiyaye Zaman Lafiya A Gaza
  • Shugabannin Kasar Australia Sun Bukaci ‘Yan Kasar Suyi Zanga Zanga Cikin Lumana
  • Shugaban Afrika Ta Kudu Yanuna Goyon Bayan Kawo Karshen Yaki Tsakanin Rasha Da Ukraine
  • Ethiopia Tana Horas Da Dakarun RSF A Wani Sansani
  • Majalisar Dottijan Najeriya Ta Amince Da Tura Sakamakon Zabe Ta Na’ura

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • Gwamnatin Bauchi: Ta Kaddamar Da Kwamitin Ma’adanai Labarai
  • Kauran Bauchi: Muna Nan A PDP Daram! Siyasa
  • Harin Makami Mai Linzami Da Rasha Ta Kai Yayi Barna Sosai A Ukraine Afrika
  • Shugaban Guinea-Bissau Umaro Na Fuskantar Matsin Lamba Afrika
  • Manya-Manyan Wasannin Wannan Makon Wasanni
  • Kasashen Duniya Sunyi Tir Da Hambarar Da Gwamnatin Venezuela Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Matsalolin Masarautun Kano Sun Kawo Karshe Najeriya
  • Babban Hafsan Tsaron Najeriya Ya Gargadi Masu Tayar Da Hankali Najeriya
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.