Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Shugaban Amurka Zai Sake Aika Jirgin Yaki Gabas Ta Tsakiya Amurka
  • Dalibin Jami’a Ya Rasa Ransa A Birnin Dakar Yayin Zanga Zanga Afrika
  • Maikaba Ya Yi Murabus A Matsayinsa Kocin Wikki Tourist FC Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • NEDC : Zata Samar Da Cikekken Kulawa Wa ‘Yan Jaridar Da Sukayi Hatsari A Bauchi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnatin Trump Zata Kafa Kasuwar Ma’adanai Amurka

Shugaba Tinubu: Naji Dadin Sako Daliban Neja Da Aka Sace
Published: December 8, 2025 at 8:03 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu ya jinjinawa hukumomin tsaro bisa kokarinsu na kubutar da dalibai 100 na makarantar Papiri Catholic School da ke Jihar Neja.

Yayin da ya bayyana farin cikinsa kan dawowar daliban cikin lafiya, Shugaba Tinubu ya kuma umarci hukumomin tsaro da su tabbatar da gaggawar kubutar da sauran dalibai 115 da malamansu da ke hannun masu garkuwa.

Shugaban Kasar ya tabbatar wa iyayen daliban cewa gwamnatin tarayya tare da gwamnatin Jihar Neja na aiki tare domin ganin an dawo da dukkan wadanda aka sace cikin koshin lafiya.

“Ina da cikakken bayani kan dawowar dalibai 100 na makarantar Catholic da ke Jihar Neja.

Ina murnar wannan cigaba tare da Gwamna Umar Bago, kuma ina yabawa hukumomin tsaro bisa jajircewarsu tun bayan mummunan lamarin da ya faru ranar 21 ga Nuwamba.

“Umarni na ga hukumomin tsaro a bayyane yake, dole ne a ceto dukkan daliban da sauran ’yan Najeriya da aka sace, a dawo da su gida lafiya sannan dole mu tabbatar da an ciro kowa ba tare da barin kowa a baya ba.

Gwamnatin tarayya za ta ci gaba da aiki tare da jihar Neja da sauran jihohi domin kara tsaro a makarantun mu da samar da mafi ingancin muhalli na ilmantarwa ga yaranmu.

“Daga yanzu, hukumomin tsaro tare da haɗin gwiwar gwamnoni dole su dakile sake faruwar irin wadannan sace sacen, ya kuma zama wajibi yaranmu su daina zama a wajajen da ’yan ta’adda za su rika kai hari don karya karatunsu da jefa kan su da iyalansu cikin bakin ciki,” in ji Shugaba Tinubu.

Labarai

Post navigation

Previous Post: Dangantaka Tayi Tsamari Tsakanin Salah Da Slot.
Next Post: An Samar Da Dala Kusan Biliyan Biyu Don Yakar Polio

Karin Labarai Masu Alaka

Gwamnatin Sham Tace Harin Kurdawa Ya Hallaka Sojojin Kasar Afrika
Hukumar Tsaron Civil Defence A Gombe Ta Samar Da Jami’ai Don Tabbatar Da Tsaro A Bukukuwan Karshen Shekara Labarai
Shugaba Trump Yace Amurka Da Iran Suna Cigaba Da Tattaunawa Amurka
Gwamna Zulum: Ya Bukaci Sojoji Su Cigaba Da Yakar Boko Haram Da ISWAP Labarai
Trump Yace Amurka Ta Kai Hare-Hare Masu Yawa Akan ‘Yan Ta’adda A Najeriya Amurka
Amurka Tafara Yiwa Kasar Iraq Barazana Amurka

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Shugaban Amurka Zai Sake Aika Jirgin Yaki Gabas Ta Tsakiya
  • Dalibin Jami’a Ya Rasa Ransa A Birnin Dakar Yayin Zanga Zanga
  • Kasar Zimbabwe Ta Samar Da Dokar Tsawaita Mulkin Mnangagwa Zuwa 2030
  • ‘Yan Bindiga Sun Karya Alkawarin Dakatar Da Kai Hare Hare A Najeriya
  • Amurka Zata Bawa Sojojin Najeriya Horo

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • CAF Ta Dakatar Da Kocin Senegal Pape Thiaw Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Kungiyar Kwadago Ta Shirya Zanga-Zanga A Najeriya Najeriya
  • ‘Yansandan Uganda Sun Tsare ‘Yar Fafutukar Kare Hakkin Bil’adama Sarah Bireete Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • An Gudanar Da Addu’oi Ga Mutane 16 Da ‘Yan Bindiga Suka Kashe a Australiya Tsaro
  • Gwamnatin Kano Zata Dauki Mataki Game Da Kisan Dorayi Tsaro
  • ‘Yan Bindiga Sun Kashe Fiye Da Mutane 15 A Kasar Australiya Labarai
  • Fiye Da Mutane 200 Sun Rasa Rayukansu A Wajen Hakar Ma’adanai Labarai
  • Dalibai Sun Koma Makarantu A Wasu Jihohin Najeriya Najeriya
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.