Shugaban Amurka Donalad Trump ya ce a yau Alhamis, ya fadawa Isra’ila kada ta sake kai hare-hare kan cibiyar iskar gas na kasar Iran, saboda musayar hare-hare da ake yi kan cibiyoyin makamashi na sa farashin su ya tashi, kuma yana kara munana yakin da ake tafkawa tsakanin Amurka Isra’ila a bangare daya da kuma Iran.
Furucin na Trump ya biyo bayan tashin gwaron zabi da farashin makamashi yayi a ranar Alhamis, bayan da Iran ta mai da martani kan harin da Isra’ila ta kai wannan babban cibiyar iskar gas ta Iran, inda ita kuma Iran din ta kai hari kan cibiyar gas ta Ras Laffan dake Qatar, wanda ke sarrafa kusan kashi 5 na gas din duniya, ta haddasa barnar da za’a dauki shekaru kafin a gyara.
Trump, wanda zai iya samun rauni a fannin siyasa tsakanin magoya bayansa saboda tsadar man fetur, yayi kakkausar magana ga ‘yan kawancen Amurka ta suka ki karban tayin sa na su taimaka a bude mashigin ruwa na Hormuz, inda ta nan ne ake tafiyar da Kashi 5 na man duniya.


