Shugaban Korea ta arewa Kin Jong Un ya halarci gwajin wani makamin linzami me dogon zango a wani wuri na gwajin makamai ranar Laraba, kamar yadda gidan jarida na kasar KCNA ya ruwaito ranar Alhamis.
An yi wannan gwajin ne, a kasar mai karfin makamashin nukiliya don a gwada fasahar samar da wani sabon makami me dogon linzami da zai iya harbo abu daga sama me nisan kilimita 200, ko mil 124 a cewar KCNA.
KCNA ta kara da cewa kirkirar wannan makami na karkashin ruwa, na daga cikin kokarin jam’iyyar me mulki a Korea ta arewa na zamanantar da sojin ta na ruwa, wanda ke cikin muhimman manufofi 5 da jam’iyyar ke son aiwatarwa don karfafa tsaro.
Kim Jong Un ya ce samar da makaman nukiliya da kuma zamanantar da sojin ruwa abu ne me muhimmanci, kuma ya zama dole saboda duniyar a yanzu ba kwanciyar hankali.


